Home Labarai ‘yan bindiga sun kai hari masallaci a jihar Kaduna

‘yan bindiga sun kai hari masallaci a jihar Kaduna

Ƴan bindiga sun kai hari kan wani masallaci a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, tare da kashe wasu masallata guda biyu.

Hukumomin ƴansanda a jihar sun tabbatar da afkuwar lamarin.

Wani shugaban al’umma a karamar hukumar, ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa ƴan bindigar sun afka wa masallacin ne a anguwar Makera da ke yankin Kwasakwasa da misalin karfe 2 ranar Juma’a, inda suka buɗe wuta kan masallatan.

Ya ce harin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum biyu.

A cewarsa, ƴan bindigar sun isa masallacin ne lokacin masu salla ke kai raka’a ta biyu, inda wasu daga cikin suka tsere.

Harin na ranar Juma’a na zuwa ne kwana guda bayan da ƴan bindiga suka sace ɗalibai 287 a wata makarantar sakandare a Kuriga da ke karamar hukumar Chikun na jihar ta Kaduna.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp