Home Labarai ‘yan Bindiga sun sace Almajirai a jihar Sokoto

‘yan Bindiga sun sace Almajirai a jihar Sokoto

Rahotannin daga jihar Sokoto na bayyana cewa wasu ‘yan bindiya dauke da makamai sun kai hari kauyen Gidan Bakuso da ke yankin karamar hukumar Gada a jihar da ke arewa maso yammacin Najeriya, tare da sace daliban wata tsangaya.

Dan majalisar tarayyar mai wakiltar yankin, Honarabul Bashir Usman Gorou ya tabbatar wa manema labarai aukuwar harin, inda ya ce kimanin dalibai 15 ne ‘yan bindigar suka sace, da wasu mata hudu.

Ya ce maharan sun far wa garin ne da tsakar daren ranar Juma’a lokacin da daliban ke barci.

Honarabul Gorou ya ce daliban almajirai ne da ke karatu a makarantar Allo wadanda shekarun suka kama daga takwas zuwa 14.

”Baya ga daliban tsangayar, dan majalisar ya ce a yanzu haka akwai fiye da mutum 63 a yankin da ke hannun ‘yan bindiga, to amma wannan shi ne karo na farko da ake sace kananan almajirai a yankin”, in ji dan majalisar.

Kakain rundunar ‘yan sandan hihar, ASP Ahmad Rufa’i, ya shaida wa BBC cewa kawo yanzu rundunar ba ta samun labarin ba, amma ta aike da jami’ata zuwa yankin don tabbatar da ainihin abin da ya faru.

Yana mai cewa zai tuntube mu da zarar ya kammala tattara bayanai daga wurin jami’ansu da ke yankin.

Harin dai na zuwa ne a yayin da yau da rana wamnatin jihar ta kaddamar da jami’an sa kai na tsaro don magance matsalar tsaron a jihar.

A baya-bayan nan ‘yan bindiga sun zafafa kai hare-hare tare da sace mutane masu yawa a wasu yankunan arewacin Najeriya.

Ko a ranar Alhamis da ta gabata ma wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari makarantar furame da karamar sakandiren Kuriga a jihar Kaduna, tare da sace daliban makarantar kimanin 287.

Haka ma makon da ya gabata wasu mahara suka sace wasu mutane mazauna sansanin ‘yan gudun hijira fiye da 100 galibinsu mata da kananan yara a lokacin da suke neman itacen girki a garin Gambouro Ngala a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp