Home Labarai ‘yan bindiga sun kai hari masallaci a jihar Kaduna

‘yan bindiga sun kai hari masallaci a jihar Kaduna

Ƴan bindiga sun kai hari kan wani masallaci a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, tare da kashe wasu masallata guda biyu.

Hukumomin ƴansanda a jihar sun tabbatar da afkuwar lamarin.

Wani shugaban al’umma a karamar hukumar, ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa ƴan bindigar sun afka wa masallacin ne a anguwar Makera da ke yankin Kwasakwasa da misalin karfe 2 ranar Juma’a, inda suka buɗe wuta kan masallatan.

Ya ce harin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum biyu.

A cewarsa, ƴan bindigar sun isa masallacin ne lokacin masu salla ke kai raka’a ta biyu, inda wasu daga cikin suka tsere.

Harin na ranar Juma’a na zuwa ne kwana guda bayan da ƴan bindiga suka sace ɗalibai 287 a wata makarantar sakandare a Kuriga da ke karamar hukumar Chikun na jihar ta Kaduna.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp