Home Labarai ‘yan bindiga sun kai hari masallaci a jihar Kaduna

‘yan bindiga sun kai hari masallaci a jihar Kaduna

Ƴan bindiga sun kai hari kan wani masallaci a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, tare da kashe wasu masallata guda biyu.

Hukumomin ƴansanda a jihar sun tabbatar da afkuwar lamarin.

Wani shugaban al’umma a karamar hukumar, ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa ƴan bindigar sun afka wa masallacin ne a anguwar Makera da ke yankin Kwasakwasa da misalin karfe 2 ranar Juma’a, inda suka buɗe wuta kan masallatan.

Ya ce harin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum biyu.

A cewarsa, ƴan bindigar sun isa masallacin ne lokacin masu salla ke kai raka’a ta biyu, inda wasu daga cikin suka tsere.

Harin na ranar Juma’a na zuwa ne kwana guda bayan da ƴan bindiga suka sace ɗalibai 287 a wata makarantar sakandare a Kuriga da ke karamar hukumar Chikun na jihar ta Kaduna.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp