Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da amincewa da tallafin naira dubu 500 ga maniyyata hajjin bana da suka fito daga jihar, a wani yunƙuri na rage masu raɗaɗin ƙarin kuɗin kujerar hajji da hukumar kula da aikin hajji ta Najeriya ta yi.
A baya-bayan nan ne hukumar alhazan ta najeriya ta sanar da ƙara kuɗin kujerar hajjin da kusan naira miliyan biyu sai dai ta bayyana cewa ƙarin bai shafi maniyyatan da ke ƙarƙashin tsarin adashin gata ba.
Read Also:
Gwamnan ya bayyana haka ne a shafinsa na X inda yace A yanzu duk maniyyaci daga jihar Kano wanda ba ya tsarin adashin gata, zai yi ƙarin naira miliyan ɗaya da dubu ɗari huɗu a maimakon sama da naira miliyan ɗaya da dubu ɗari tara.
Ya ce “duk maniyyacin da ya yi rajista kuma ya biya kafin alƙalamin naira miliyan 4.7 da naira miliyan 4.5 a hukumar alhazai ta jiha a yanzu zai biya naira miliyan 1.4 a maimakon naira miliyan 1.9.”
To sai dai sanarwar gwamnan ba ta fayyace ko tallafin zai kasance ga dukkannin maniyyatan jihar ba ne ko kuma wadanda ba za su iya yin cikon ba.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1486 days 18 hours 54 minutes 59 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1468 days 20 hours 36 minutes 24 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com