Home Labarai Rundunar Sojin saman Nijeriya ta kone jiragen ruwan dakon Danyen Mai a...

Rundunar Sojin saman Nijeriya ta kone jiragen ruwan dakon Danyen Mai a Neja Delta

Dakarun sojin saman Najeriya da ke aiki ƙarƙashin rundunar ‘Operation Delta Safe’ sun sami nasarar tarwatsa wuraren tace mai ba bisa ƙa’ida ba da jiragen ruwan dakon kaya maƙare da ɗanyen mai da aka sace a yankin Neja Delta.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin saman Najeriya, Edward Gabkwet, ya fitar wadda ta ce a yayin wani samame da dakarun suka kai kan cibiyoyin da jiragen ruwan dakon kayan tsakanin 25 da 26 ga watan Maris a wasu yankunan jihar Rivers.

An gano wani jirgin dakon kaya a yankin Bille cike da albarkatun mai da aka tace ba bisa ƙa’ida ba. Kazalika, sojojin a yankin Dariama da Tumakiri, wuraren da suka yi suna kan tace mai ba bisa ƙa’ida ba, sojojin sun gano tukwanen girki abin da ke nuna akwai mutane a wajen. Sun kuma yi musayar wuta tsakaninsu inda kuma suka lalata wuraren da ake tace man ba bisa doka ba.

A cewar sanarwar, sojoji sun ƙona wasu wuraren da aka gano ana tace ɗanyen mai ba bisa ƙa’ida ba inda kuma aka cinna masu wuta.

A baya, sojoji sun lalata wuraren da aka gano a Bille da Dariama. Rundunar sojin saman da wasu hukumomin tsaro, a cewar sanarwar za su ci gaba da ƙara ƙaimi wajen gano ayyukan masu satar ɗanyen ma da ke gudanar da ayyukansu a yankin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp