Home Labarai Rundunar Sojin saman Nijeriya ta kone jiragen ruwan dakon Danyen Mai a...

Rundunar Sojin saman Nijeriya ta kone jiragen ruwan dakon Danyen Mai a Neja Delta

Dakarun sojin saman Najeriya da ke aiki ƙarƙashin rundunar ‘Operation Delta Safe’ sun sami nasarar tarwatsa wuraren tace mai ba bisa ƙa’ida ba da jiragen ruwan dakon kaya maƙare da ɗanyen mai da aka sace a yankin Neja Delta.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin saman Najeriya, Edward Gabkwet, ya fitar wadda ta ce a yayin wani samame da dakarun suka kai kan cibiyoyin da jiragen ruwan dakon kayan tsakanin 25 da 26 ga watan Maris a wasu yankunan jihar Rivers.

An gano wani jirgin dakon kaya a yankin Bille cike da albarkatun mai da aka tace ba bisa ƙa’ida ba. Kazalika, sojojin a yankin Dariama da Tumakiri, wuraren da suka yi suna kan tace mai ba bisa ƙa’ida ba, sojojin sun gano tukwanen girki abin da ke nuna akwai mutane a wajen. Sun kuma yi musayar wuta tsakaninsu inda kuma suka lalata wuraren da ake tace man ba bisa doka ba.

A cewar sanarwar, sojoji sun ƙona wasu wuraren da aka gano ana tace ɗanyen mai ba bisa ƙa’ida ba inda kuma aka cinna masu wuta.

A baya, sojoji sun lalata wuraren da aka gano a Bille da Dariama. Rundunar sojin saman da wasu hukumomin tsaro, a cewar sanarwar za su ci gaba da ƙara ƙaimi wajen gano ayyukan masu satar ɗanyen ma da ke gudanar da ayyukansu a yankin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp