Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan bindiga 11 a jihohin Katsina da Zamfara

Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan bindiga 11 a jihohin Katsina da Zamfara

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarun da ta tura don aikin murƙushe ‘yan ta-da-ƙayar-baya a jihohin Katsina da Zamfara sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga 11 a cikin kwana biyu.

Sun dai kai samame ne maɓoyar waɗanda suka kira ‘yan ta’adda, inda suka kashe wani adadi na ‘yan bindigar a ranar 29 ga watan Maris.

Ta ce dakarun soji sun yi nasarar kai wa mafakar wani riƙaƙƙen ɗan fashin daji mai suna Hassan ‘Yan tagwaye hari, a cikin ƙaramar hukumar Tsafe, inda suka kashe uku a cikinsu tare da ƙwato makamai.

Rundunar sojin ta kuma ce dakarunta sun ragargaza sansanonin ɗan fashin, wanda ta ce yana da hannu wajen satar mutane da ayyukan ta’addanci a wasu yankuna na arewa maso yamma.

A jihar Katsina kuma, cewar rundunar sojin ƙasan Najeriya, dakarunta sun gwabza faɗa a ranar 30 ga watan Maris da waɗanda suka kira ‘yan ta’adda a Shawu Kuka da Shinda da Tafki da Gidan Surajo da Citakushi da Kabai I da Kabai II duka a cikin ƙaramar hukumar Faskari.

Ta ce dakarun sun yi nasarar kashe ‘’yan ta’adda’ takwas tare da gano bindigogi ƙirar gida guda uku da kakin sojoji da kuma ɗumbin hatsin sata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp