Home Labarai Gwamnatin jihar Zamfara ta musanta batun ciyo bashin Naira Biliyan 14.26

Gwamnatin jihar Zamfara ta musanta batun ciyo bashin Naira Biliyan 14.26

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa ba ta ciyo rancen kuɗi naira biliyan 14.26 ba, sai dai kuɗin wani ɓangare ne na kuɗaɗen da gwamnatin da ta shuɗe ta ciyo na naira biliyan 20.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin jihar ta Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, inda ya ce gwamnati ba ta ci wani bashi a gida ko waje ba tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal.

A makon jiya ne hukumar kula da basuka ta Najeriya ta fitar da rahoto game da gwamnonin da suka ci bashi a cikin wata shida.

Rahoton ya ce sababbin gwamnonin jihohi 13 na ƙasar ciki har da Kano, da Zamfara, da Katsina da Sokoto da Kaduna sun ci bashin naira biliyan 226 daga masu bayar da bashi a ciki da wajen ƙasar, bayan rantsar da su a watan Mayun 2023.

Hukumar ta kuma ce ta haɗa alƙaluman ne bayan jimillar lissafin da suka yi kan farashin dala a kan naira 889.

Amma gwamnatin jihar Zamfara ta musanta hakan inda ta ce, “Muna so mu fayyace rahoton ofishin kula da basuka (DMO) cewa gwamnatin jihar Zamfara ta ciyo bashin Naira biliyan 14.26.

“Gwamnatin jihar Zamfara ba ta taɓa neman buƙatar karɓar rance ba ko tuntuɓar majalisar jiha ko ta ƙasa domin neman wannan buƙata,” in ji sanarwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp