Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan bindiga 11 a jihohin Katsina da Zamfara

Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan bindiga 11 a jihohin Katsina da Zamfara

Soji

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarun da ta tura don aikin murƙushe ‘yan ta-da-ƙayar-baya a jihohin Katsina da Zamfara sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga 11 a cikin kwana biyu.

Sun dai kai samame ne maɓoyar waɗanda suka kira ‘yan ta’adda, inda suka kashe wani adadi na ‘yan bindigar a ranar 29 ga watan Maris.

Ta ce dakarun soji sun yi nasarar kai wa mafakar wani riƙaƙƙen ɗan fashin daji mai suna Hassan ‘Yan tagwaye hari, a cikin ƙaramar hukumar Tsafe, inda suka kashe uku a cikinsu tare da ƙwato makamai.

Rundunar sojin ta kuma ce dakarunta sun ragargaza sansanonin ɗan fashin, wanda ta ce yana da hannu wajen satar mutane da ayyukan ta’addanci a wasu yankuna na arewa maso yamma.

A jihar Katsina kuma, cewar rundunar sojin ƙasan Najeriya, dakarunta sun gwabza faɗa a ranar 30 ga watan Maris da waɗanda suka kira ‘yan ta’adda a Shawu Kuka da Shinda da Tafki da Gidan Surajo da Citakushi da Kabai I da Kabai II duka a cikin ƙaramar hukumar Faskari.

Ta ce dakarun sun yi nasarar kashe ‘’yan ta’adda’ takwas tare da gano bindigogi ƙirar gida guda uku da kakin sojoji da kuma ɗumbin hatsin sata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp