Sojojin Saman Nijeriya sun sake hallaka Kwamandan ISWAP a Jihar Borno

Nigeria Airforce

Wani harin dakarun sojin saman Nijeriya karkashin Operation Hadin kai (OPHK) yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar mayakan kungiyar ISWAP a kauyen Kulleram dake yankin tafkin Chadi.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar mai dauke da kwanan wata 16 ga watan Afrilun 2024.

Sanarwar ta ce dakarun sun gudanar da harin ne a ranar 13 ga watan Afrilun 2024, wanda yayi sanadiyyar mutuwar mayakan masu tada kayar baya kimanin 30, wanda cikin su harda manyan kwamandoji da suka hadar da Ali Dawud, Bakura Fallujah, da Malla Ari.

Haka kuma yayin harin dakarun sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan, baburan hawa da wasu kayan aikin ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Rahotannin sirri dake fitowa daga yankin na kulleram wanda ke matsayin  wata cibiyar hada-hada wanda ciki har da sarrafa kayan masarufi.

Sanarwar tace atisayen rundunar sojin saman ya nuna yadda runudnar sojin ta mayar da hankali wajen ganin ta kawar da  matsalolin rashin tsaro dake addabar Al’ummar Nijeriya.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 28 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 10 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com