Home Labarai Gwamnatin Kano zata sake gurfanar da Ganduje bisa zargin Almundahana

Gwamnatin Kano zata sake gurfanar da Ganduje bisa zargin Almundahana

Hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta ce zata sake gurfanar da tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje bisa zargin almundahana da almubazzaranci da dukiyoyin al’umma.

Shugaban hukumar, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana hakan a yayin wata ganawa da gidan talabijin na Channels Television ta cikin shirin (Sunrise Daily).

“Yanzu haka da nake magana da ku, muna kan binciken wasu kudin har kimanin N51.3bn wadanda gwamnatin tarayya ta turowa kananan hukumomi kuma aka dauke su daga asusun gwamnati aka aika wa wasu mutane, kuma mun gano mutanen da aka turawa kudin.”

Magaji ya yi zargin cewa a watan karshe na gwamnatin Ganduje ta kwashi Naira biliyan 1 daga asusun gwamnati, da sunan za’a yi aikin hanya da su, amma sai muka ga an tura da kudin ga wasu kamfanonin Chanji Kudaden kasashen waje.

“Muna da wata kara da muka shigar akan Naira biliyan 4, wadda aka fitar da ita daga asusun ajiyar kudaden shiga na jihar Kano zuwa wani kamfanin noma. Duk wadannan kararraki suna gaban kotu,” inji shi.

Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa na Kano, wanda ya ce ana kallonsa a matsayin “mai taurin kai” saboda harkar halasta kudaden haramun batu ne da gwamnatin tarayya ce da hurumi akai, amma yace hukumarsa na da hakkin bincike akan zargin almundahana da ake yiwa Ganduje .

Magaji yace ya fara binciken gwamnatin Ganduje ne tun yana gwamnan Kano. Ya ce bai kamata a samu shafaffu da mai a yaki da cin hanci da rashawa a jihar ba.

“Abun dadin shi ne kyawun a Najeriya ba Wanda ya Isa yace yafi karfin a gurfanar da shi a gaban Shari’ar don haka kawai Ganduje ya shirya gurfana a gaban kotu domin ya kare kansa.”

Idan za’a iya tunawa kadaura24, gwamnatin jihar kano za ta gurfanar da Ganduje a ranar Laraba 17 ga Afrilu, 2024, bisa tuhumar da ake masa na cin hanci da rashawa, karkatar da kudade, da almubazzaranci da wasu kudade da suka hada da zargin karbar cin hanci da rashawa $413,000 da kuma N1.38bn.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp