Home Labarai Sojojin Saman Nijeriya sun sake hallaka Kwamandan ISWAP a Jihar Borno

Sojojin Saman Nijeriya sun sake hallaka Kwamandan ISWAP a Jihar Borno

Nigeria Airforce

Wani harin dakarun sojin saman Nijeriya karkashin Operation Hadin kai (OPHK) yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar mayakan kungiyar ISWAP a kauyen Kulleram dake yankin tafkin Chadi.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar mai dauke da kwanan wata 16 ga watan Afrilun 2024.

Sanarwar ta ce dakarun sun gudanar da harin ne a ranar 13 ga watan Afrilun 2024, wanda yayi sanadiyyar mutuwar mayakan masu tada kayar baya kimanin 30, wanda cikin su harda manyan kwamandoji da suka hadar da Ali Dawud, Bakura Fallujah, da Malla Ari.

Haka kuma yayin harin dakarun sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan, baburan hawa da wasu kayan aikin ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Rahotannin sirri dake fitowa daga yankin na kulleram wanda ke matsayin  wata cibiyar hada-hada wanda ciki har da sarrafa kayan masarufi.

Sanarwar tace atisayen rundunar sojin saman ya nuna yadda runudnar sojin ta mayar da hankali wajen ganin ta kawar da  matsalolin rashin tsaro dake addabar Al’ummar Nijeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp