Sojojin Nijeriya Sun tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Zamfara

Sojojin Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a karamar hukumar Maru dake jihar Zamfara.

Wannan na kushe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar sojojin Nijeriya Manjo Janar Onyema Nwachukwu, wadda ya fitar ranar talaka aka raba ga manema labarai.

Sanarwar tace dakarun sojin sun yi nasara hallaka ‘yan ta’adda 12 a karamar hukumar ta Maru, tare da tarwatsa maboyar su, bayan samun wasu bayanan sirri da suka kan ‘yan bindigar.

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun hallaka mayakan 12 bayan musayar wuta da su yi, in da wasu kuma suka tsere cikin daji da raunin  harbi a jukkunan su.

Haka kuma dakarun sojin sun sami nasarar kwato bindiga kirar AK 47, baburan hawa, bindiga kirar gida da sauran muggan makamai.

Jihar Zamfara na guda cikin jihohin arewacin Nijeriya dake fama da matsalar rashin tsaro, sakamakon ‘yan bindiga masu satar mutane domin karbar kudin fansa, wadanda ke aukawa garuruwan jihar.

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 17 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 59 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com