Home Labarai Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Wata babbar kotu a jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Idan dai za’a iya tunawa kwanaki biyu da suka gabata ne shugabancin APC na mazabar Ganduje a Karamar Hukumar Dawakin Tofa, mahaifar Ganduje, ya dakatar da shi bisa zargin cin-hanci da rashawa da gwamnatin Kano ke yi masa.

Ta cikin umarnin kotun, ƙarƙashin Mai Shari’a Usman Na’abba, ta hana Ganduje, wanda shine tsohon gwamnan Kano, nuna kan sa a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

Na’abba ya kuma hana Ganduje yin wani taro ko daukar mataki a matsayin shugaban jam’iyyar har sai an kammala zaman sauraron karar.

Ya kuma hana shugabancin jam’iyyar na jiha shiga cikin maganar da take gaban kotu.

Dr. Ibrahim Sa’ad, a madadin biyu daga cikin shugabannin APC na mazabar Ganduje, mataimakin sakatare, Laminu Sani da mai baiwa jam’iyyar shawara kan harkokin Shari’a, Haladu Gwanjo ne ya shigar da karar.

Haka kuma kotun ta umarci waɗanda ake kara su hudu da suka haɗa da jam’iyar APC a matakin kasa da jiha da kuma shi Ganduje din da su tsaya a matsayin su daga 15 ga Afrilu zuwa 30 ga watan Afrilu lokacin da za a saurari karar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp