Home Labarai Gwamnatin Kano ta bada Umarnin Rufe wasu tituna a jihar

Gwamnatin Kano ta bada Umarnin Rufe wasu tituna a jihar

Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta bayar da umarnin aikin gina katafariyar Gadar ƙasa (Underpass tare da Gadar Sama, Flyover) a shataletalen Tal’udu.

A bisa buƙatar kammala wannan muhimmin aiki cikin lokacin da aka tsara, gwamnati ta ba wa Ɗan kwangila umarnin fara wannan aikin nan take.

Domin samun damar yin aiki cikin nustuwa da kwanciyar hankali, za a rufe sassan titin Muhammad Abdullahi Wase daga ranar Alhamis 18/4/2024.

wannan na kunshe ta cikin wata sanar mai dauke da sa hannun  kwamishin ma’ikatar ayyuka da gidaje na jihar Engr. Marwan Ahmed Aminu, MNSE.

A bisa buƙatar sauƙaƙa zirga-zirga ga masu ababen hawa, ma’aikatar ayyuka da gidaje ta jihar Kano ta samu nasarar samarwa tare da gyaran hanyoyin da za a yi amfani da su domin kyaucewa wurin da aka rufe.

An samar da titunan yanke ta cikin unguwanni kamar haka:

1- Titin Muhammad Abdullahi Wase (Rahama Street zuwa titin Aminu Kano (W.A.A RANO Filling Station).

2- Titin Aminu Kano zuwa titin Muhammad Abdullahi Wase (Kusa da makarantar Adamu na Ma’aji).

3- Titin Muhammad Abdullahi Wase (Layin Nufawa zuwa titin Aminu Kano, layin Mai Tangaran).

4- Titin Aminu Kano (Shaho Street zuwa titin Muhammad Abdullahi Wase).

Haka kuma ana shawartar masu ababen hawa da su nisanci wurin da ake gudanar da wannan katafaren aiki idan ba ya zama dole ba, domin samun zirga-zirga cikin nutsuwa kuma rage cunkoso.

Gwamnatin jihar Kano tana ƙara neman goyon baya tare da haɗin kan jama’a domin samun nasarar wannan aiki da zai inganta rayuwarmu, bunƙasa kasuwanci tare da kyautata zirga-zirga cikin yanayi mai sauƙi.

Muna godiya tare da jinjina ga jama’ar Kano bisa soyayya, addu’o’i, goyon baya tare da ƙwarin guiwa da ku ke ba wa mai girma gwamna da gwamnatinsa.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp