Home Labarai Sojojin Nijeriya sun bankado maboyar mayakan ISWAP a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun bankado maboyar mayakan ISWAP a jihar Borno

Rundunar sojojin Najeriya ta ce dakarunta sun sami nasarar bankado maboyar mayakan boko haram tsagin ISWAP a jihar Borno dake Arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Onyema Nwachukwa ya fitar aka raba manema labarai.

Sanarwar ta ce dakarun rundunar karkashin “operation Desert Sanity III” sun kai wani harin ta sama da kuma makaman atilare a hannu guda da wasu dakru na musamman a kauyukan Ngumne, kawaran da Mangu dake dajin sambisa da yankin Timbuktu.

Yace dakarun sojin sun yi bata-kashi da mayakan boko haram inda suka yi amfani da wasu makamai masu fashewa kan mayakan na ISWAP, wannan ta sanya suka ci karfin mayakan inda suka ranta a na kare.

Nwachukwa ya kara da cewa dakarun sojin sun sami nasarar kwato manyan makamai, da suka hadar da motar dake daukan bindigu, bindigar kirar 105mm howitzer, haka kuma sun tarwatsa maboyar mayakan na ISWAP.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp