Home Labarai Sojojin Nijeriya sun bankado maboyar mayakan ISWAP a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun bankado maboyar mayakan ISWAP a jihar Borno

Rundunar sojojin Najeriya ta ce dakarunta sun sami nasarar bankado maboyar mayakan boko haram tsagin ISWAP a jihar Borno dake Arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Onyema Nwachukwa ya fitar aka raba manema labarai.

Sanarwar ta ce dakarun rundunar karkashin “operation Desert Sanity III” sun kai wani harin ta sama da kuma makaman atilare a hannu guda da wasu dakru na musamman a kauyukan Ngumne, kawaran da Mangu dake dajin sambisa da yankin Timbuktu.

Yace dakarun sojin sun yi bata-kashi da mayakan boko haram inda suka yi amfani da wasu makamai masu fashewa kan mayakan na ISWAP, wannan ta sanya suka ci karfin mayakan inda suka ranta a na kare.

Nwachukwa ya kara da cewa dakarun sojin sun sami nasarar kwato manyan makamai, da suka hadar da motar dake daukan bindigu, bindigar kirar 105mm howitzer, haka kuma sun tarwatsa maboyar mayakan na ISWAP.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp