Home Labarai An janye ‘Yansandan dake samar da tsaro ga hukumar dake bincikar Ganduje...

An janye ‘Yansandan dake samar da tsaro ga hukumar dake bincikar Ganduje a Kano

Babban sufeton ƴan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya janye ƴan sanda kimanin 40 da ke samar wa hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe da yaƙi da rashawa ta jihar Kano tsaro.

Matakin ya zo ne bayan binciken badaƙalar kuɗi da hukumar, ƙarƙashin jagorancin Muhuyi Magaji Rimin Gado take yi kan shugaban jam’iyyar APC ta ƙasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa babban sufeton ƴan sandan ya bayar da umarnin janye ƴan sandan ga kwamishinan yan sanda na jihar Kano, Usaini Gumel.

Wata majiya da jaridar ta ruwaito ta ce wasu cikin ƴan sandan suna taimaka wa hukumar ta yaƙi da rashawa a Kano a binciken da take yi tare da samar da tsaro ga hedikwatar hukumar da sauran dukiyoyin da ake bincike a kansu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp