Home Labarai ‘Yansanda a jihar Bauchi sun hallaka ‘yan Ta’adda takwas

‘Yansanda a jihar Bauchi sun hallaka ‘yan Ta’adda takwas

Ƴan sanda tare da haɗin gwiwar ƙungiyar mahauta a Bauchi sun kashe mutum takwas da ake zargin masu garkuwa da mutane ne yayin musayar wuta a kusa da iyakar jihar da Filato.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda ta jihar Bauchi SP Ahmed Wakil ya bayyana wa ƴan jarida a jihar a ranar Alhamis cewa ƴan sanda sun samu nasarar ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su don karɓar kuɗin fansa.

Sanarwa da mai magana da yawun hukumar ya fitar ta bayyana cewa “Jami’an na ƴan sanda da aka kawo daga offisoshin ƴan sanda na Gumau da Tilde da Tulu sun haɗu da masu garkuwa da mutane tare da makamansu yayin da suke bakin aikinsu na tabbatar da tsaro inda suka yi musayar wuta da ya yi sanadiyyar kashe masu garkuwar huɗu.

“Biyu daga cikin waɗanda ake zargin da suka mutu daga bisani sun amsa laifin garkuwa da mutane da dama a Bauchi da Filato da ya haɗa da mummunan kisan gillar da aka yi wa maigarin Ruruwai a garin Lame dake ƙaramar hukumar Toro.

“Yayin musayar bindiga tsakanin jami’an da sauran masu garkuwar da ke gadin mutanen da aka yi garkuwa da su aka sake kashe mutum huɗu cikinsu sannan aka samu ƙwato mutum ukun da ke hannunsu ba tare da biyan kuɗin fansa ba”.

SP Wakil ya yi kira ga al’umomin garuruwan Bauchi da su ba da haɗin kai da jami’an tsaron ta hanyar samar musu da bayanan sirri da za su taimaka wajen shawo kan matsalolin tsaro kafin ma su faru wanda faruwar tasu kan iya samar da mummunan lahani a kan rayuka da kuma dukiyoyi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp