Home Labarai ‘Yansanda a jihar Bauchi sun hallaka ‘yan Ta’adda takwas

‘Yansanda a jihar Bauchi sun hallaka ‘yan Ta’adda takwas

Ƴan sanda tare da haɗin gwiwar ƙungiyar mahauta a Bauchi sun kashe mutum takwas da ake zargin masu garkuwa da mutane ne yayin musayar wuta a kusa da iyakar jihar da Filato.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda ta jihar Bauchi SP Ahmed Wakil ya bayyana wa ƴan jarida a jihar a ranar Alhamis cewa ƴan sanda sun samu nasarar ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su don karɓar kuɗin fansa.

Sanarwa da mai magana da yawun hukumar ya fitar ta bayyana cewa “Jami’an na ƴan sanda da aka kawo daga offisoshin ƴan sanda na Gumau da Tilde da Tulu sun haɗu da masu garkuwa da mutane tare da makamansu yayin da suke bakin aikinsu na tabbatar da tsaro inda suka yi musayar wuta da ya yi sanadiyyar kashe masu garkuwar huɗu.

“Biyu daga cikin waɗanda ake zargin da suka mutu daga bisani sun amsa laifin garkuwa da mutane da dama a Bauchi da Filato da ya haɗa da mummunan kisan gillar da aka yi wa maigarin Ruruwai a garin Lame dake ƙaramar hukumar Toro.

“Yayin musayar bindiga tsakanin jami’an da sauran masu garkuwar da ke gadin mutanen da aka yi garkuwa da su aka sake kashe mutum huɗu cikinsu sannan aka samu ƙwato mutum ukun da ke hannunsu ba tare da biyan kuɗin fansa ba”.

SP Wakil ya yi kira ga al’umomin garuruwan Bauchi da su ba da haɗin kai da jami’an tsaron ta hanyar samar musu da bayanan sirri da za su taimaka wajen shawo kan matsalolin tsaro kafin ma su faru wanda faruwar tasu kan iya samar da mummunan lahani a kan rayuka da kuma dukiyoyi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp