Mayakan ISWAP sun Hallaka DPO a Jihar Borno

Rahotannin daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa wasu da ake zargin mayakan kungiyar boko haram tsagin ISWAP sun hallaka baturen dan sanda Sunday Pius a karamar hukumar Marte dake jihar.

Haka kuma harin ‘yan ta’addan yayi sanadiyyar raunata wasu jami’an ‘yan sanda guda biyu.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da faruwa lamarin ta bakin Kakakin ta ASP Kenneth Daso ya a birnin Maiduguri a yammacin ranar talata.

ASP Kenneth yace sun sami kiran gaggawa cewa ‘yan ta’addan sun hallaka baturen ‘yan sanda dake lura da yankin New Marte a ranar Litinin wannan ne ya sanya kwamishinan ‘yan sandna jihar ya bada umarni yin bincike.

An ruwaito cewa mayakan sun shiga cikin garin ne da misalign karfe 7 da mintuna 30 na daren ranar litinin, in da suka kai hari kan jami’an lafiya, sai dai an ruwaito jami’an lafiyar sun tsallake rijiya da baya.

Bayan da jami’an lafayar sukayi gudun tsira zuwa ofishin ‘yan sandan ne ‘yan ta’addan suka afkawa ofishin nan suka hallaka baturen ‘yan sandan tare da raunata jami’an ‘yan sanda guda biyu.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 24 minutes 47 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 6 minutes 12 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com