Home General Kotu ta dakatar da Dawo da Sunusi Lamido sarautar Kano

Kotu ta dakatar da Dawo da Sunusi Lamido sarautar Kano

Babbar kotun tarayya a jihar kano ta bada umarnin dawo da sarkin Kano Muhammadu Sunusi kan karagar mulkin masarautar jihar.

Mai shari’a AM liman ne ya bayar da umarnin gaggauta dakatarwa ga gwamnatin jihar, bayan bayan wata kara da sarkin Dawaki Babba, Aminu Babba dan Agundi ya shigar gaban kotun.

Alhaji Aminu Babba Dan Agundi ya yi karar Rukunonin guda 8 da suka haɗar da Gwamnatin jihar kano, Majalisar dokokin jihar, Kakakin Majalisar dokokin jihar, Kwamishinan Shari’ar na Kano, Kwamishinan yan sandan jihar, Babban sufeton yan sandan Nigeria , Civil Defense, da kuma hukumar DSS.

Idan dai za’a iya tunawa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar ta 2024 bayan da majalisar dokoki ta soke dukkan masarautun jihar biyar da aka ƙirƙira a shekarar 2019.

Jim kaɗan bayan rattaba hannu a kan dokar, gwamnan ya sanar da naɗa Khalifa Muhammadu Sanusi II a matsayin sabon Sarkin Kano na 16, bayan ya sauke Aminu Ado Bayero daga kan kujerar.

Matakin kuma ya nuna cewa an soke masarautun Gaya da Bichi da Ƙaraye da kuma na Rano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp