Kotu ta dakatar da Dawo da Sunusi Lamido sarautar Kano

Babbar kotun tarayya a jihar kano ta bada umarnin dawo da sarkin Kano Muhammadu Sunusi kan karagar mulkin masarautar jihar.

Mai shari’a AM liman ne ya bayar da umarnin gaggauta dakatarwa ga gwamnatin jihar, bayan bayan wata kara da sarkin Dawaki Babba, Aminu Babba dan Agundi ya shigar gaban kotun.

Alhaji Aminu Babba Dan Agundi ya yi karar Rukunonin guda 8 da suka haɗar da Gwamnatin jihar kano, Majalisar dokokin jihar, Kakakin Majalisar dokokin jihar, Kwamishinan Shari’ar na Kano, Kwamishinan yan sandan jihar, Babban sufeton yan sandan Nigeria , Civil Defense, da kuma hukumar DSS.

Idan dai za’a iya tunawa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar ta 2024 bayan da majalisar dokoki ta soke dukkan masarautun jihar biyar da aka ƙirƙira a shekarar 2019.

Jim kaɗan bayan rattaba hannu a kan dokar, gwamnan ya sanar da naɗa Khalifa Muhammadu Sanusi II a matsayin sabon Sarkin Kano na 16, bayan ya sauke Aminu Ado Bayero daga kan kujerar.

Matakin kuma ya nuna cewa an soke masarautun Gaya da Bichi da Ƙaraye da kuma na Rano.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 58 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 40 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com