Home General Kwankwaso – bani da Hannu a rushe masarautun Kano

Kwankwaso – bani da Hannu a rushe masarautun Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP a Najeriya kuma tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ba shi da hannu a rushe masarautun jihar da gwamnatinsu ta yi ranar Alhamis.

Ana yi wa Kwankwaso kallon babban jagora kuma mafi ƙarfin faɗa-a-ji a ɓangaren siyasar Kwankwasiyya na jam’iyyar NNPP, wadda ke mulkin Kanon a yanzu.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya rushe masarautun biyar ne bayan ‘yan majalisar dokokin jihar sun rushe dokar da magabatansu suka ƙirƙira a 2019 ƙarƙashin gwamnatin Abdullahi Ganduje ta jam’iyyar APC.

Soke dokar ta sa aka tuɓe duka sarakunan jihar biyar kuma nan take gwamnan ya bayyana sunan Muhammadu Sanusi II (ko kuma Sanusi Lamido Sanusi) a matsayin sabon sarki bayan masu naɗin sarki sun zaɓe shi.

ta cikin tattaunawa da yayi da manema labarai kwankwaso ya bayyana cewa yanzu haka yana Abuja kawai labarin ya samu kamar yadda kowa ya gani a kafafen yada labarai

“Ni dai ga ni a Abuja, abin da ka gani ni ma shi na gani,”

Ya ƙara da cewa sai a ranar Juma’a ne yake sa ran zuwa birnin na Kano, wadda za ta iya yin daidai da ranar da Sarki Muhammadu Sanusi II zai koma kan karagar mulkin Kano.

“Zan yi magana da ‘yan majalisar da shi gwamnan don mu ji yadda abubuwan suke,” in ji shi.

Sai dai tun a watan Janairun da ya gabata Kwankwaso ya tabbatar da cewa babu shakka za a sake nazari kan dokar da ta kafa sabbin masarautun huɗu a Kano.

“Gaskiya yana ɗaya daga cikin abubuwan da ba a taɓa zama da ni a kai ba, amma kuma nasan dole za a zo a yi magana,” kamar yadda ya bayyana a lokacin.

“Da ma ba cewa na yi a yi dama ko a yi hagu ba, cewa na yi za a duba kuma ga shi sun duba.”

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp