Home General Kwankwaso – bani da Hannu a rushe masarautun Kano

Kwankwaso – bani da Hannu a rushe masarautun Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP a Najeriya kuma tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ba shi da hannu a rushe masarautun jihar da gwamnatinsu ta yi ranar Alhamis.

Ana yi wa Kwankwaso kallon babban jagora kuma mafi ƙarfin faɗa-a-ji a ɓangaren siyasar Kwankwasiyya na jam’iyyar NNPP, wadda ke mulkin Kanon a yanzu.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya rushe masarautun biyar ne bayan ‘yan majalisar dokokin jihar sun rushe dokar da magabatansu suka ƙirƙira a 2019 ƙarƙashin gwamnatin Abdullahi Ganduje ta jam’iyyar APC.

Soke dokar ta sa aka tuɓe duka sarakunan jihar biyar kuma nan take gwamnan ya bayyana sunan Muhammadu Sanusi II (ko kuma Sanusi Lamido Sanusi) a matsayin sabon sarki bayan masu naɗin sarki sun zaɓe shi.

ta cikin tattaunawa da yayi da manema labarai kwankwaso ya bayyana cewa yanzu haka yana Abuja kawai labarin ya samu kamar yadda kowa ya gani a kafafen yada labarai

“Ni dai ga ni a Abuja, abin da ka gani ni ma shi na gani,”

Ya ƙara da cewa sai a ranar Juma’a ne yake sa ran zuwa birnin na Kano, wadda za ta iya yin daidai da ranar da Sarki Muhammadu Sanusi II zai koma kan karagar mulkin Kano.

“Zan yi magana da ‘yan majalisar da shi gwamnan don mu ji yadda abubuwan suke,” in ji shi.

Sai dai tun a watan Janairun da ya gabata Kwankwaso ya tabbatar da cewa babu shakka za a sake nazari kan dokar da ta kafa sabbin masarautun huɗu a Kano.

“Gaskiya yana ɗaya daga cikin abubuwan da ba a taɓa zama da ni a kai ba, amma kuma nasan dole za a zo a yi magana,” kamar yadda ya bayyana a lokacin.

“Da ma ba cewa na yi a yi dama ko a yi hagu ba, cewa na yi za a duba kuma ga shi sun duba.”

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp