Home General Tinubu ya taya ‘yan Nijeriya murna cika shekaru 25 a tirbar Damukradiyya

Tinubu ya taya ‘yan Nijeriya murna cika shekaru 25 a tirbar Damukradiyya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa tana cika alƙawurran da ta yi wa jama’ar kasar.

Tinubu wanda ya taya ƴan Najeriya murnar cika shekara 25 kan mulkin dimokuraɗiyya babu katsewa, ya kuma nemi haɗin kan al’umma domin samar da kyakkyawar ƙasa da za ta zamo abin alfahari ga ƴan baya.

Ya kuma yi gargaɗi a kan jefa dimokuraɗiyya cikin mawuyacin hali yana mai cewa “Dole mu ci gaba da haɗa kai wajen gina ƙasarmu da kuma jaddadawa a koda yaushe, cewa ba mu da wata ƙasa da ta fi Najeriya’’.

A wani jawabi da ya yi wa majalisar dokokin Najeriya, shugaba Tinubu ya nemi haɗin kan ƴan majalisar da ma sauran jama’ar ƙasar wajen ci gaba da aiwatar da manufofin gwamnatinsa da kuma bunƙasa Najeriya.

Shugaban Najeriyar ya kuma nemi goyon bayan majalisar wajen kammala aiki a kan kasafin kuɗin da ya gabatar mata, wanda ya ce zai taimaka wajen aiwatar da tsare-tsaren da gwamnati ke da su, masu muhimmanci ga jama’ar ƙasa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp