Home General Kungiyoyin Kwadagon Nijeriya sun janye yajin aiki

Kungiyoyin Kwadagon Nijeriya sun janye yajin aiki

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago biyu a Najeriya, wato Nigeria Labour Congress da kuma Trade Union Congress sun sanar da dakatar da yajin aikin da suka fara yi a ranar Litinin.

Ƙungiyoyin biyu sun sanar da wannan mataki ne bayan kammala tattaunawar shugabannin ƙungiyoyin biyu yau Talata, a Abuja.

Ƙungiyoyin ƙwadagon sun tsunduma yajin aiki ne bayan gaza cimma matsaya tsakaninsu da gwamnatin tarayya kan abin da zai zama albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikata a Najeriya.

Jim kaɗan bayan kammala taron, ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce sun janye yajin aikin ne domin hanzarta tattaunawar da ake yi tsakanin su da gwamnati game da albashi mafi ƙanƙanta, wanda shi ne babban abin da ya janyo taƙaddamar.

Zaman da shugabannin NLC da TUC suka yi a ranar ta Talata ya mayar da hankali ne kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyoyin da gwamnatin a wata ganawa da suka yi ranar Talata tare da sakataren gwamnatin tarayya.

Yajin aikin dai ya taɓa ɓangarori daban-daban na tattalin arziƙin Najeriya, ɗaya daga ciki shi ne katsewar lantarki a faɗin ƙasar.

Tun farko, a ranar Talata ƙungiyar ta bayyana cewa za ta ci gaba da yajin aikin har sai shugabannin ƙungiyar sun kammala tattaunawa kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyar da gwamnati.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp