Home General Gwamnatin Nijeriya tace ‘yan Nijeriya zasu wahala saboda yajin aikin NLC da...

Gwamnatin Nijeriya tace ‘yan Nijeriya zasu wahala saboda yajin aikin NLC da TUC

Ministar ƙwadago ta Najeriya, Nkeiruka Onyejeocha, ta ce ƴan ƙasar zasu sha wuya idan har ƙungiyar ƙwadago ta NLC, ta kafe kan ci gaba da yajin aikin da suka kira.

ta bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da ita a tashar talabijin ta Channels, bayan da shugabannin ƙwadagon suka jagoranci yajin aiki na sai baba ta gani daga ranar Litinin, a kan maganar mafi ƙanƙantar albashi a Najeriya.

Ministar ta ce tana fatan za a samu matsaya a kan batun albashin, amma tafiya yajin aiki abu ne da ke tattare da illoli ga tattalin arziƙin ƙasa da kuma rayuwar jama’a.

Onyejeocha ta ce, ”idan yajin aikin ya ci gaba, ƴan ƙasa za su wahala, kuma tuni ma har sun fara wahala. Ɗalibanmu da ya kamata su rubuta jarrabawa lamarin ya shafe su saboda sun rasa ababen hawa da za su je wuraren jarrabawar.”

Ta ƙara da cewa, ”akwai kuma mutanen da ba su da abin da za su ci sai sun je wuraren aikinsu sun nema. Wasu mutanen da ke aiki a sakatariya kullum sun dogara ne a kan abin da suke samu a ofisoshin.”

”Sannan a ɓangaren yin ayyuka da abubuwa, mun san cewa idan aka dakatar da ayyuka, hakan zai shafe tattalin arziƙinmu,” in ji ministar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp