Home General Gwamnatin Nijeriya tace ‘yan Nijeriya zasu wahala saboda yajin aikin NLC da...

Gwamnatin Nijeriya tace ‘yan Nijeriya zasu wahala saboda yajin aikin NLC da TUC

Ministar ƙwadago ta Najeriya, Nkeiruka Onyejeocha, ta ce ƴan ƙasar zasu sha wuya idan har ƙungiyar ƙwadago ta NLC, ta kafe kan ci gaba da yajin aikin da suka kira.

ta bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da ita a tashar talabijin ta Channels, bayan da shugabannin ƙwadagon suka jagoranci yajin aiki na sai baba ta gani daga ranar Litinin, a kan maganar mafi ƙanƙantar albashi a Najeriya.

Ministar ta ce tana fatan za a samu matsaya a kan batun albashin, amma tafiya yajin aiki abu ne da ke tattare da illoli ga tattalin arziƙin ƙasa da kuma rayuwar jama’a.

Onyejeocha ta ce, ”idan yajin aikin ya ci gaba, ƴan ƙasa za su wahala, kuma tuni ma har sun fara wahala. Ɗalibanmu da ya kamata su rubuta jarrabawa lamarin ya shafe su saboda sun rasa ababen hawa da za su je wuraren jarrabawar.”

Ta ƙara da cewa, ”akwai kuma mutanen da ba su da abin da za su ci sai sun je wuraren aikinsu sun nema. Wasu mutanen da ke aiki a sakatariya kullum sun dogara ne a kan abin da suke samu a ofisoshin.”

”Sannan a ɓangaren yin ayyuka da abubuwa, mun san cewa idan aka dakatar da ayyuka, hakan zai shafe tattalin arziƙinmu,” in ji ministar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp