Home General Kungiyoyin Kwadagon Nijeriya sun janye yajin aiki

Kungiyoyin Kwadagon Nijeriya sun janye yajin aiki

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago biyu a Najeriya, wato Nigeria Labour Congress da kuma Trade Union Congress sun sanar da dakatar da yajin aikin da suka fara yi a ranar Litinin.

Ƙungiyoyin biyu sun sanar da wannan mataki ne bayan kammala tattaunawar shugabannin ƙungiyoyin biyu yau Talata, a Abuja.

Ƙungiyoyin ƙwadagon sun tsunduma yajin aiki ne bayan gaza cimma matsaya tsakaninsu da gwamnatin tarayya kan abin da zai zama albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikata a Najeriya.

Jim kaɗan bayan kammala taron, ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce sun janye yajin aikin ne domin hanzarta tattaunawar da ake yi tsakanin su da gwamnati game da albashi mafi ƙanƙanta, wanda shi ne babban abin da ya janyo taƙaddamar.

Zaman da shugabannin NLC da TUC suka yi a ranar ta Talata ya mayar da hankali ne kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyoyin da gwamnatin a wata ganawa da suka yi ranar Talata tare da sakataren gwamnatin tarayya.

Yajin aikin dai ya taɓa ɓangarori daban-daban na tattalin arziƙin Najeriya, ɗaya daga ciki shi ne katsewar lantarki a faɗin ƙasar.

Tun farko, a ranar Talata ƙungiyar ta bayyana cewa za ta ci gaba da yajin aikin har sai shugabannin ƙungiyar sun kammala tattaunawa kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyar da gwamnati.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp