Home General CBN ya bayyana dalilin Kwace lasisin Bankin Heritage

CBN ya bayyana dalilin Kwace lasisin Bankin Heritage

Babban bankin Nijeriya CBN ya kwace lasisin bankin Haeritage, wanda dakatarwar ta fara aiki nan take.

Wannan na kunshe ta cikin wata takardar sanarwa da mukaddashin daraktan yada labarai ta bankin ta fitar Hakama Sidi Ali, inda tace wannan mataki na zuwa ne bayan da bankin ya karya wasu dokoki na BOFIA.

Ta cikin sanarwa babban bankin na CBN yace bankin ya sabawa sashi na 12 (1) na dokar

“Bankin da hukumar gudanarwasa sun gaza habaka fannin kudin su, wanda ke barazana ga tattalin arzikin kasar nan. Duk da bibiya da CBN yayi domin taimakon bankin, amma bankin Heritage ya cigaba da gudanar da ayyukan sa ba tare da ya dauki matakan gyara ba, A cewar babban bankin na CBN

Domin tabbatar da kwarin gwiwa da gaskiya a fannin harkokin kudi bankin na CBN da hukumar NDIC sun dauki matakin kwace lasisin bankin dogaro da sashe na 12 (2) na dokar BOFIA 2020.

Hakan kuma babban bankin na CBN ya tabbatarwa da ‘yan Nijeriya cewa fannin harkokin kudi zai cigaba da habaka da samun ingantaccen tsaro.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp