Home General CBN ya bayyana dalilin Kwace lasisin Bankin Heritage

CBN ya bayyana dalilin Kwace lasisin Bankin Heritage

Babban bankin Nijeriya CBN ya kwace lasisin bankin Haeritage, wanda dakatarwar ta fara aiki nan take.

Wannan na kunshe ta cikin wata takardar sanarwa da mukaddashin daraktan yada labarai ta bankin ta fitar Hakama Sidi Ali, inda tace wannan mataki na zuwa ne bayan da bankin ya karya wasu dokoki na BOFIA.

Ta cikin sanarwa babban bankin na CBN yace bankin ya sabawa sashi na 12 (1) na dokar

“Bankin da hukumar gudanarwasa sun gaza habaka fannin kudin su, wanda ke barazana ga tattalin arzikin kasar nan. Duk da bibiya da CBN yayi domin taimakon bankin, amma bankin Heritage ya cigaba da gudanar da ayyukan sa ba tare da ya dauki matakan gyara ba, A cewar babban bankin na CBN

Domin tabbatar da kwarin gwiwa da gaskiya a fannin harkokin kudi bankin na CBN da hukumar NDIC sun dauki matakin kwace lasisin bankin dogaro da sashe na 12 (2) na dokar BOFIA 2020.

Hakan kuma babban bankin na CBN ya tabbatarwa da ‘yan Nijeriya cewa fannin harkokin kudi zai cigaba da habaka da samun ingantaccen tsaro.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp