Home General Yajin aikin da ƴan kwadago ke yi ya saɓa wa doka –...

Yajin aikin da ƴan kwadago ke yi ya saɓa wa doka – Gwamnatin Najeriya

Ministan shari’a na Najeriya Lateef Fagbemi ya ce yajin aikin da manyan ƙungiyoyin ƙwadagon ƙasar suka fara a ranar litinin kan mafi ƙanƙantar albashi ya saɓa wa doka.

Babban lauyan na gwamnati ya bayyana hakan ne bisa dalilin cewa ƙungiyoyin ba su bi ka’idojin da dokar ƙwadago ta gindaya ba.

wannan dai na zuwa ne bayan manyan kungiyoyin ma’aikata biyu na NLC da TUC, suka fara yajin aikin sai baba-ta-gani daga Litinin bayan gwamnati ta gaza cika wa’adin ranar 31 ga watan Mayu na aiwatar da ƙarin albashi mafi ƙanƙanta da kuma rage farashin wutar lantarki.

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta NLC da TUC sun ce za a fara yajin aikin har sai sun sami sabon albashi mafi ƙanƙanta na ƙasa kuma har sai gwamnati ta yi da gaske.

Ƙungiyoyin ƙwadagon na son a sanya albashi mafi ƙanƙanta kan dala $334, kwatankwacin N494,000 kenan inda kuma gwamnati ta tsaya a kan Naira 30,000, kwatankwacin dala 22, duk wata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp