Home General Yajin aikin da ƴan kwadago ke yi ya saɓa wa doka –...

Yajin aikin da ƴan kwadago ke yi ya saɓa wa doka – Gwamnatin Najeriya

Ministan shari’a na Najeriya Lateef Fagbemi ya ce yajin aikin da manyan ƙungiyoyin ƙwadagon ƙasar suka fara a ranar litinin kan mafi ƙanƙantar albashi ya saɓa wa doka.

Babban lauyan na gwamnati ya bayyana hakan ne bisa dalilin cewa ƙungiyoyin ba su bi ka’idojin da dokar ƙwadago ta gindaya ba.

wannan dai na zuwa ne bayan manyan kungiyoyin ma’aikata biyu na NLC da TUC, suka fara yajin aikin sai baba-ta-gani daga Litinin bayan gwamnati ta gaza cika wa’adin ranar 31 ga watan Mayu na aiwatar da ƙarin albashi mafi ƙanƙanta da kuma rage farashin wutar lantarki.

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta NLC da TUC sun ce za a fara yajin aikin har sai sun sami sabon albashi mafi ƙanƙanta na ƙasa kuma har sai gwamnati ta yi da gaske.

Ƙungiyoyin ƙwadagon na son a sanya albashi mafi ƙanƙanta kan dala $334, kwatankwacin N494,000 kenan inda kuma gwamnati ta tsaya a kan Naira 30,000, kwatankwacin dala 22, duk wata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp