Home General Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar Dokokin jihar Kano ta musanta labarin dake cewa tayi jinkirin komawa aiki ne, saboda barazanar tsaron da take fuskanta akan dambarwar Masarautar jihar.
Kakakin Majalisar Dokokin Kano Rt, Honarabul Jibril Ismail Falgore ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Kamaluddeen Sani Shawai ya aiko wa PRNigeria a safiyar Laraba, sanar ta ce wannan labarin bashi da tushe ballantana makama.
A cewar Falgore “wannan labari ne mai haɗari da wasu mutane ke yaɗawa wanda ke cewa, mun ƙi komawa zaman majalisa saboda barazanar tsaron da muke fuskanta akan dambarwar masarautar Kano ba gaskiya bane, domin kuwa babu wani labari makamancin wannan koma mai kama da shi”. inji Falgore.
Sanarwar ta kuma ayyana ranar 15 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata dawo daga hutun da tayi, domin ci-gaba da samar da managartan ƙudirirrikan da zasu dace da manufofin Gwamnatin Kano, ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusif na ciyar da Jihar gaba.
A ƙarshe sanarwar ta yi fatan al’umma zasuyi watsi da wancan labari da ake yaɗawa, kuma su ci-gaba da yin addu’oin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a lungu da saƙo na jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp