Home DUNIYA Kotu a Abuja ta dage saurarar karar da ake bukatar Ganduje ya...

Kotu a Abuja ta dage saurarar karar da ake bukatar Ganduje ya sauka daga shugabancin APC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a Najeriya ta sake dage sauraren karar da ke neman a tsige tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasar har zuwa ranar 5 ga watan Yuli.

Mai shari’a Inyang Ekwo, a ranar Laraba, ya dage ci gaba da zama sauraron karar a karo na biyu domin baiwa mai kara damar amsa sabuwar bukatar da Ganduje ya shigar na kalubalantar cancantar karar.

A zaman na Laraba, lauyan mai kara, Benjamin Davou, ya shaida wa kotun cewa Sanusi Musa, SAN, wanda ke kare Ganduje, ya mika masa wata sabuwar bukata.

Ya ce zai bukaci lokaci don yin nazari kan ko zai amsa takardar. Lauya Musa bai yi adawa da bukatar Davou na dage zaman ba.

A saboda haka mai shari’a Ekwo ya dage ci gaba da sauraron karar har sai ranar 5 ga watan Yuni domin ci gaba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp