Home DUNIYA Majalisar Dokokin Kaduna ta Magantu kan karar da El’Rufa’i ya shigar

Majalisar Dokokin Kaduna ta Magantu kan karar da El’Rufa’i ya shigar

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta yi watsi da karar da tsohon gwamnan jihar Malam Nasir El-Rufai ya shigar gaban wata kotun tarayya inda yake kalubalantar rahoton Majalisar da ya zarge shi da almundahana da kuɗin gwamnati a lokacin mulkinsa.

Shi dai tsohon gwamnan na zargin Majalisar ne da take masa hakki kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanadar.

Majalisar ta musanta cewa an take masa hakki a bincikenta.

Ita dai Majalisar dokokin jihar Kaduna a martanin da ta mayar, ta ce ta yi matukar mamaki ne yadda tsohon gwamnan ya ruga zuwa kotu, yana kalubalantar sakamakon binciken da kwamitinta ya gudanar, tana mai cewa yin hakan tamkar riga Malam Masallaci ne.

Mai magana da yawun Majalisar dokokin jihar Kaduna, Hon Henry Maraa, ya ce an mika rahoton ne domin a ci gaba da bincike kuma “za a kira shi”.

Game da zargin El Rufai na rashin ba shi dama domin kare kansa kuwa, Hon Maraa ya kara da cewa “za a bashi dama, za a kira shi, abin da muka lura da shi shi ne wadanda suka sa hannu da wadanda suka karbi kudi, da wadanda suka ba da kudi, idan an je gaba, idan an yi bincike idan an je kan shi, za a kira shi.”

Sai dai ya ce akwai abin mamaki a ce a yanzu tsohon gwamnan yana zuwa kotu “El Rufai da bai martaba kotu ba a wayi gari shi yake zuwa kotu.”

Ya dage cewa babu kuskure a binciken da suka yi sannan za su zauna da lauyoyinsu sannan kuma su mayar masa da martani.

A nasa bangaren, Mohammad Lawal, kakakin gwamna Uba Sani na jihar Kaduna, ya ce takaddamar da ake ciki tsakanin El Rufai da sauran jami’an gwamnatinsa da kuma majalisar dokokin jihar Kaduna ta kunshi abubuwa da yawa – zargi da badakala.

“Ba za a yi saurin yanke hukunci ba, sai an zauna an bincika abin, sannan a gwamnatance ba wannan aikin kawai muka sa a gaba ba, ana samun wadanda suke cewa a bincika, ana samun wadanda suke cewa ba su yadda ba.” in ji shi.

Ya kara da cewa “ba za a hada baki da mu a cuci talakan jihar Kaduna ba.” kamar yadda kakakin ya bayyana.

A cewarsa, an kafa kwamitin bisa tsarin doka don haka ya ce bai kamata ace masu doka a gwamnatin dimokradiyya na take dokokin da suka ba da yancin fadin albarkacin baki ba.

“Abin da muke nema shi ne kotu ta yi watsi da wannan rahoto saboda ya take masa hakki.” in ji Malam Jafaru Sani.

Wannan al’amari na binciken tsohon gwamnan jihar Kadunan dai shi ne gaba-gaba cikin batutuwan da jama’a da dama a jihar ke tafka muhawara a kai, wani abu da wasu masana ke cewa manuniyace na irin wainar da za a toya a fagen siyasar jihar a zaben 2027.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp