Home DUNIYA Maitamakin shugaban hukumar Kwastom ya mutu a zauren majalisar wakilai

Maitamakin shugaban hukumar Kwastom ya mutu a zauren majalisar wakilai

Rahoyanin daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa mataimakin Shugaban hukumar hana fasa kwari ta Kasa dake lura da harkokin kudi da gudanarwa Essien Etop Andrew ya yanke jiki ya fadi a gaban zauren Majalisar wakilan Nijeriya.

A yayin da yake amsa tambayoyin a gaban ‘yan majalisar wakilan Andrew ya sarke, wannan ne ya sanya shi faduwa kasa magashiyyan.

Jaridar Solacebase ta ruwaito cewa masu bayar da agajin gaggawa na majalisar sun garzaya da shi asibiti amma abin yaci tura ya kai ga  mutuwar sa.

Ta cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun majalisar wakilan Akin Rotimi, ya fitar ta ce majalisar zata bayar da gudunmawar don ganin an fahimci lamari da abinda ke kewaye da shi ga dukkanin masu ruwa da tsaki.

Haka kuma ta ce kakakin majalisar Tajuddeen Abbas, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalai da hukumar ta NCS, yace majalisar ta damu matuka da mutuwar jami’an

Bamidele Salam wanda shike jagorantar Kwamitin dake bincike ya ce kwamitin ya dage zaman zuwa mako guda domin girmama marigayin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp