Home General Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar Dokokin jihar Kano ta musanta labarin dake cewa tayi jinkirin komawa aiki ne, saboda barazanar tsaron da take fuskanta akan dambarwar Masarautar jihar.
Kakakin Majalisar Dokokin Kano Rt, Honarabul Jibril Ismail Falgore ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Kamaluddeen Sani Shawai ya aiko wa PRNigeria a safiyar Laraba, sanar ta ce wannan labarin bashi da tushe ballantana makama.
A cewar Falgore “wannan labari ne mai haɗari da wasu mutane ke yaɗawa wanda ke cewa, mun ƙi komawa zaman majalisa saboda barazanar tsaron da muke fuskanta akan dambarwar masarautar Kano ba gaskiya bane, domin kuwa babu wani labari makamancin wannan koma mai kama da shi”. inji Falgore.
Sanarwar ta kuma ayyana ranar 15 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata dawo daga hutun da tayi, domin ci-gaba da samar da managartan ƙudirirrikan da zasu dace da manufofin Gwamnatin Kano, ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusif na ciyar da Jihar gaba.
A ƙarshe sanarwar ta yi fatan al’umma zasuyi watsi da wancan labari da ake yaɗawa, kuma su ci-gaba da yin addu’oin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a lungu da saƙo na jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp