Home General Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar Dokokin jihar Kano ta musanta labarin dake cewa tayi jinkirin komawa aiki ne, saboda barazanar tsaron da take fuskanta akan dambarwar Masarautar jihar.
Kakakin Majalisar Dokokin Kano Rt, Honarabul Jibril Ismail Falgore ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Kamaluddeen Sani Shawai ya aiko wa PRNigeria a safiyar Laraba, sanar ta ce wannan labarin bashi da tushe ballantana makama.
A cewar Falgore “wannan labari ne mai haɗari da wasu mutane ke yaɗawa wanda ke cewa, mun ƙi komawa zaman majalisa saboda barazanar tsaron da muke fuskanta akan dambarwar masarautar Kano ba gaskiya bane, domin kuwa babu wani labari makamancin wannan koma mai kama da shi”. inji Falgore.
Sanarwar ta kuma ayyana ranar 15 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata dawo daga hutun da tayi, domin ci-gaba da samar da managartan ƙudirirrikan da zasu dace da manufofin Gwamnatin Kano, ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusif na ciyar da Jihar gaba.
A ƙarshe sanarwar ta yi fatan al’umma zasuyi watsi da wancan labari da ake yaɗawa, kuma su ci-gaba da yin addu’oin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a lungu da saƙo na jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp