Home General Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar dokokin kano ta mangantu kan jinkirin komawarta bakin aiki

Majalisar Dokokin jihar Kano ta musanta labarin dake cewa tayi jinkirin komawa aiki ne, saboda barazanar tsaron da take fuskanta akan dambarwar Masarautar jihar.
Kakakin Majalisar Dokokin Kano Rt, Honarabul Jibril Ismail Falgore ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Kamaluddeen Sani Shawai ya aiko wa PRNigeria a safiyar Laraba, sanar ta ce wannan labarin bashi da tushe ballantana makama.
A cewar Falgore “wannan labari ne mai haɗari da wasu mutane ke yaɗawa wanda ke cewa, mun ƙi komawa zaman majalisa saboda barazanar tsaron da muke fuskanta akan dambarwar masarautar Kano ba gaskiya bane, domin kuwa babu wani labari makamancin wannan koma mai kama da shi”. inji Falgore.
Sanarwar ta kuma ayyana ranar 15 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata dawo daga hutun da tayi, domin ci-gaba da samar da managartan ƙudirirrikan da zasu dace da manufofin Gwamnatin Kano, ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusif na ciyar da Jihar gaba.
A ƙarshe sanarwar ta yi fatan al’umma zasuyi watsi da wancan labari da ake yaɗawa, kuma su ci-gaba da yin addu’oin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a lungu da saƙo na jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp