Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar –...

Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar – Lagbaja

Shugaban sojojin Nijeriya Laftanal Janar Taoreed Lagbaja yace dakarun dake yaki da ayyukan ta’addanci da sauran lamaurran da suka shafi tsaro a yankin Arewa maso gabashin kasar na samun gagarumar nasara.

Lagbaja ya bayyana hakan ne a ranar alhamis a garin Jos, yayin da yake ganawa da manema labarai, a wani bangare na bikin cikar shekara da rundunar ta shirya.

ya dora alhakin harin kunar baki wake a Gwozo bisa hare haren da dakarun sojoji suka din gi kaiwa kan mabambanta gungun ‘yan ta’addan a yakin na arewa maso gaba.

yace: “Ana sake samun nasarori bisa yadda dakarun ke cigaba da matsa kaimi da kuma wasu hare hare kan ‘yan ta’addan dake yankin.

Ya kara da cewa sun sami bayanan sirri dake nuna yadda ‘yan Ta’addan suka shirya kai hare-hare kunar bakin wake har guda 15 amma 3 ne kawai suka sami nasara.

“Dakrun mu sun yi dukkanin mai yiwuwa don gani sun kawar da makiya.

“Don haka, ina kira ga Al’ummar Nijeriya da su zama masu taimakawa harkokin tsaro, zamu tabbatar da bincikar dukkanin wani taron al’umma,” a cewar sa.

ya bayyana yaki da rashin tsaro matsayin abinda ke bukatar hada karfi da karfe, “don haka ya kamata mu dauke shi da matukar muhimmanci”.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp