Home DUNIYA Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin kwadagon na NLC da TUC sun sake tabbatarwa da shugaban kasa Bola Tinubu matsayar su kan mafi karancin albashi naira 250,000.

Jaridar Politics Digest ta ruwaito Shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar su da shugaban kasar a fadar sa dake birnin tarayya Abuja, inda yace sun tsaya kai da fata kan mafi karancin albashin ma’aikatan.

Tinubu yace yana bukatar lokaci domin yin nazari gami da tuntubar masu ruwa da tsaki, kafin aika kudirin mafi karancin albashin ga majalisar kasa.

da yake ganawa da manema labaran a ranar alhamis Ajearo da wasu shuwagabannin kungiyoyin kwadago na kasar, yace shuwagannin kwadagon sun zo ne su tattauna ba daidaitawa ba.

inda yace ganawar zata cigaba mako na gaba.

bayan ganawar ta tsahon sa’a, shuwagabannin kungiyoyin kwadagon sun fito bisa rakiyar shugaban kasa, inda suka fadawa ‘yan jarida cewa zasu koma zuwa ga mutane kafin daga bisani su dawo fadar shugaban kasar.

Shugaban kungiyar YUC Festos Osifo, yace bayan sun gama bayyana matsayar ta su shima shugaban kasa yayi bayani, duk dai bai bayyana abin da Tinubun ya fada a yayin ganawar ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp