Home DUNIYA Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin kwadagon na NLC da TUC sun sake tabbatarwa da shugaban kasa Bola Tinubu matsayar su kan mafi karancin albashi naira 250,000.

Jaridar Politics Digest ta ruwaito Shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar su da shugaban kasar a fadar sa dake birnin tarayya Abuja, inda yace sun tsaya kai da fata kan mafi karancin albashin ma’aikatan.

Tinubu yace yana bukatar lokaci domin yin nazari gami da tuntubar masu ruwa da tsaki, kafin aika kudirin mafi karancin albashin ga majalisar kasa.

da yake ganawa da manema labaran a ranar alhamis Ajearo da wasu shuwagabannin kungiyoyin kwadago na kasar, yace shuwagannin kwadagon sun zo ne su tattauna ba daidaitawa ba.

inda yace ganawar zata cigaba mako na gaba.

bayan ganawar ta tsahon sa’a, shuwagabannin kungiyoyin kwadagon sun fito bisa rakiyar shugaban kasa, inda suka fadawa ‘yan jarida cewa zasu koma zuwa ga mutane kafin daga bisani su dawo fadar shugaban kasar.

Shugaban kungiyar YUC Festos Osifo, yace bayan sun gama bayyana matsayar ta su shima shugaban kasa yayi bayani, duk dai bai bayyana abin da Tinubun ya fada a yayin ganawar ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp