Home General Yadda Gwamnatin Jihar Borno ta karbi Tubabbun ‘Yan Boko Haram 8,490 a...

Yadda Gwamnatin Jihar Borno ta karbi Tubabbun ‘Yan Boko Haram 8,490 a jihar

Gwamnatin Jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya ta ce ta sami nasarar karbar tubabbun mayakan kungiyar boko haram 8,490 ta hanya shirin sabunta jihar Borno wato  (Borno modern).

Kwamishinan yada labaran jihar farfesa Usman Tar ne ya bayyana hakan yayin da ake bawa tubabbun mayakan 560 rantsuwar tuba a birnin maiduguri a ranar laraba.

yace wannan sanannen al’mari ne ga dakarun sojojin da sauran jami’an tsaro dama masu rike da sarautun gargajiya a jihar.

yace shirin na tafiya yadda yakamata sannan kuma sun kama kwamiti domin bindiddigi, inda ya tabbatar da cewa wadanda suka tuban basa sake  komawa ruwa tare da karya dokoki, sai dai suna komawa harkokin su na kasuwanci ne ma.

shima da yake jawabi a yayin  taron mashawarci na musamman kan harkokin tsaro ga Gwamnan Jihar Birgediya Janar Abdullahi Ishaq (mai ritaya), ya tabbatar da adadin inda yace zuwa yanzu gwamantin jihar ta sami nasarar karbar tubabbun mayakan da suka kai 8,490, wanda hakan ya rage hadarin da al’ummar jihar ke fuskanta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp