Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya karkashin dakarun Operation WHIRL STROKE (OPWS) sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa a tsaunin Adamu Katibu dake karamar hukumar Lau ta jihar Taraba.

Wannan na matsayin matakin da rundunar ke dauka na kawar da ayyukan ta’addanci da suka addabi sassan kasar.

atisayen ya gudanane bayan wasu bayanan sirri da dakarun suka samu, hadin gwiwa da wasu dakarun tsaro a kasar, kan maboyar ta ‘yan ta’addan a yankin, inda suka yi musayar wuta daga bisani wasu cikin su suka tsere.

sai dai dakarun sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda uku daga cikin su, wadanda suka hadar da Haruna Buba mai kimanin shekaru (20), Hassan kakale mai shekaru da Hussaini kakale dukkansu masu shekaru (28) da haihuwa.

a yayin atisayen dakarun sun sami nasarar kubutar da Hauwa’u Alhaji Umaru da kuma Asma’u Alhaji Umaru da suka yi garkuwa da su tun a ranar 7 ga watan Yunin 2024, wanda tuni an kai su shalkwatar dakarun sojin dake ta 6 Brigade domin duba lafiyar su inda daga bisani za’a mika su ga ahlinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp