Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya karkashin dakarun Operation WHIRL STROKE (OPWS) sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa a tsaunin Adamu Katibu dake karamar hukumar Lau ta jihar Taraba.

Wannan na matsayin matakin da rundunar ke dauka na kawar da ayyukan ta’addanci da suka addabi sassan kasar.

atisayen ya gudanane bayan wasu bayanan sirri da dakarun suka samu, hadin gwiwa da wasu dakarun tsaro a kasar, kan maboyar ta ‘yan ta’addan a yankin, inda suka yi musayar wuta daga bisani wasu cikin su suka tsere.

sai dai dakarun sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda uku daga cikin su, wadanda suka hadar da Haruna Buba mai kimanin shekaru (20), Hassan kakale mai shekaru da Hussaini kakale dukkansu masu shekaru (28) da haihuwa.

a yayin atisayen dakarun sun sami nasarar kubutar da Hauwa’u Alhaji Umaru da kuma Asma’u Alhaji Umaru da suka yi garkuwa da su tun a ranar 7 ga watan Yunin 2024, wanda tuni an kai su shalkwatar dakarun sojin dake ta 6 Brigade domin duba lafiyar su inda daga bisani za’a mika su ga ahlinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp