Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya karkashin dakarun Operation WHIRL STROKE (OPWS) sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa a tsaunin Adamu Katibu dake karamar hukumar Lau ta jihar Taraba.

Wannan na matsayin matakin da rundunar ke dauka na kawar da ayyukan ta’addanci da suka addabi sassan kasar.

atisayen ya gudanane bayan wasu bayanan sirri da dakarun suka samu, hadin gwiwa da wasu dakarun tsaro a kasar, kan maboyar ta ‘yan ta’addan a yankin, inda suka yi musayar wuta daga bisani wasu cikin su suka tsere.

sai dai dakarun sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda uku daga cikin su, wadanda suka hadar da Haruna Buba mai kimanin shekaru (20), Hassan kakale mai shekaru da Hussaini kakale dukkansu masu shekaru (28) da haihuwa.

a yayin atisayen dakarun sun sami nasarar kubutar da Hauwa’u Alhaji Umaru da kuma Asma’u Alhaji Umaru da suka yi garkuwa da su tun a ranar 7 ga watan Yunin 2024, wanda tuni an kai su shalkwatar dakarun sojin dake ta 6 Brigade domin duba lafiyar su inda daga bisani za’a mika su ga ahlinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp