Home DUNIYA Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin kwadagon na NLC da TUC sun sake tabbatarwa da shugaban kasa Bola Tinubu matsayar su kan mafi karancin albashi naira 250,000.

Jaridar Politics Digest ta ruwaito Shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar su da shugaban kasar a fadar sa dake birnin tarayya Abuja, inda yace sun tsaya kai da fata kan mafi karancin albashin ma’aikatan.

Tinubu yace yana bukatar lokaci domin yin nazari gami da tuntubar masu ruwa da tsaki, kafin aika kudirin mafi karancin albashin ga majalisar kasa.

da yake ganawa da manema labaran a ranar alhamis Ajearo da wasu shuwagabannin kungiyoyin kwadago na kasar, yace shuwagannin kwadagon sun zo ne su tattauna ba daidaitawa ba.

inda yace ganawar zata cigaba mako na gaba.

bayan ganawar ta tsahon sa’a, shuwagabannin kungiyoyin kwadagon sun fito bisa rakiyar shugaban kasa, inda suka fadawa ‘yan jarida cewa zasu koma zuwa ga mutane kafin daga bisani su dawo fadar shugaban kasar.

Shugaban kungiyar YUC Festos Osifo, yace bayan sun gama bayyana matsayar ta su shima shugaban kasa yayi bayani, duk dai bai bayyana abin da Tinubun ya fada a yayin ganawar ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp