Home DUNIYA Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin Kwadago a Nijeriya sun gana da Tinubu

Kungiyoyin kwadagon na NLC da TUC sun sake tabbatarwa da shugaban kasa Bola Tinubu matsayar su kan mafi karancin albashi naira 250,000.

Jaridar Politics Digest ta ruwaito Shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar su da shugaban kasar a fadar sa dake birnin tarayya Abuja, inda yace sun tsaya kai da fata kan mafi karancin albashin ma’aikatan.

Tinubu yace yana bukatar lokaci domin yin nazari gami da tuntubar masu ruwa da tsaki, kafin aika kudirin mafi karancin albashin ga majalisar kasa.

da yake ganawa da manema labaran a ranar alhamis Ajearo da wasu shuwagabannin kungiyoyin kwadago na kasar, yace shuwagannin kwadagon sun zo ne su tattauna ba daidaitawa ba.

inda yace ganawar zata cigaba mako na gaba.

bayan ganawar ta tsahon sa’a, shuwagabannin kungiyoyin kwadagon sun fito bisa rakiyar shugaban kasa, inda suka fadawa ‘yan jarida cewa zasu koma zuwa ga mutane kafin daga bisani su dawo fadar shugaban kasar.

Shugaban kungiyar YUC Festos Osifo, yace bayan sun gama bayyana matsayar ta su shima shugaban kasa yayi bayani, duk dai bai bayyana abin da Tinubun ya fada a yayin ganawar ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp