Kudirin kirkiro sabuwar jihar Etiti a Najeriya ya tsallake karatu na biyu

Ƙudirin da ke neman ƙirƙiro sabuwar jiha a yankin kudu maso gabashin Najeriya ya tsallake karatu na biyu a Majalisar Wakilai.

Ƙudirin yana neman a ƙara jihar Etiti a yankin mai jihohi biyar kuma ‘yanmajalisa Amobi Ogah (LP, Abia), Miriam Onuoha (APC, Imo), Kama Nkemkama (LP, Ebonyi), Chinwe Nnabuife (YPP, Anambra), da kuma Anayo Onwuegbu (LP, Enugu) ne suka gabatar da shi.

Ogah ya ce niyyarsu ita ce kawo ƙarshen abin da aka daɗe ana tattauna a kai na yawan jihohi a yankin nasu. Suna so ne a yanki jihar daga jihohin yankin na Anambra, Imo, Ebonyi, Abia, and Enugu.

Yayin zaman na jiya Alhamis, an amince da ƙudirin ne a mataki na biyu ba tare da wata muhawara ba daga ‘yanmajalisar, inda suka amsa amincewa lokacin da Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas ya nemi kaɗa ƙuri’a da baki.

A ranar Laraba ma Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila ya gabatar da ƙudirin neman ƙirƙiro jihar Tiga daga Kano a arewa maso yammacin ƙasar.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 40 minutes 22 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 21 minutes 47 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com