Tinubu ya nada sabon shugaban Hukumar NPA

Shugaban kasa Bola Tinubu ya naɗa Abubakar Ɗantsoho matsayin sabon Shugaban Hukumar Tashoshin Ruwa ta NPA.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Kasa, Ajuri Ngelale ya fitar a Yammacin Juma’ar.

Naɗin Ɗantsoho na zuwa ne bayan sallamar Mohammed Bello-Koko daga shugabancin hukumar tashoshin ruwa kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Kazalika, sanarwar ta ce Tinubu ya kuma naɗa tsohon Sanatan Ekiti ta Kudu kuma tsohon Ƙaramin Ministan Ayyuka, Dayo Adeyeye a matsayin sabon Shugaban Majalisar Gudanarwar hukumar ta NPA.

Kafin naɗinsa, Ɗantsoho ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar ciki har da muƙamin babban manaja ne hukumar ta NPA.

Dukkan su za su fara aiki ne nan take, kamar yadda sanarwar Fadar Shugaban Kasar ta bayyana.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 23 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 4 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com