Home DUNIYA Tinubu ya nada sabon shugaban Hukumar NPA

Tinubu ya nada sabon shugaban Hukumar NPA

Shugaban kasa Bola Tinubu ya naɗa Abubakar Ɗantsoho matsayin sabon Shugaban Hukumar Tashoshin Ruwa ta NPA.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Kasa, Ajuri Ngelale ya fitar a Yammacin Juma’ar.

Naɗin Ɗantsoho na zuwa ne bayan sallamar Mohammed Bello-Koko daga shugabancin hukumar tashoshin ruwa kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Kazalika, sanarwar ta ce Tinubu ya kuma naɗa tsohon Sanatan Ekiti ta Kudu kuma tsohon Ƙaramin Ministan Ayyuka, Dayo Adeyeye a matsayin sabon Shugaban Majalisar Gudanarwar hukumar ta NPA.

Kafin naɗinsa, Ɗantsoho ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar ciki har da muƙamin babban manaja ne hukumar ta NPA.

Dukkan su za su fara aiki ne nan take, kamar yadda sanarwar Fadar Shugaban Kasar ta bayyana.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp