Home DUNIYA Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin jihar Kano ta yi alƙawarin kammala aikin gyara dukkannin cibiyoyin koyar da sana,oin dogaro da Kai da kuma kirkire-kirkire Wanda tsohon Gwamna Rabi’u Musa kwankwaso ya Samar tun a shekarar 2011 a daukacin ƙananan hukumomi 44 da ke Kano.

Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin bikin ranar baje kolin fasahar matasa ta duniya da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake ƙaramar hukumar Dawakin kudu haɗin gwiwa da hukumar kula da ilimin ƙananan yara ta duniya UNESCO ta shirya.

Gwamnan ya ce yin riko da sana’o’in hannu zai taimaka wajen habaka tattalin arziki da Kuma samawa Matasa aikin yi.

Abba Kabir ya yi alkawarin samawa cibiyar da gidajen kwanan dalibai da biya musu kudin karatu da daukar nauyin kai su makaranta a kullum da kuma kulawa da walwalarsu.

Da ya ke jawabi a wajen taron karamin ministan ma’aikatar ci-gaban matasa Mista Ayodele Olawode ya yaba da harkokin cibiyar, inda ya ce ma’aikatar sa ta fito da wani shirin ilimantar da matasa miliyan 7 sana’o’in dogaro da kai.

Shugaban Hukumar UNESCO a Nijeriya Abdulrahman Diyalo ya ce za su yi haɗin gwiwa da gwamnatin kano da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote domin koyar da dubban matasa sana’o’in dogaro da kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp