Home DUNIYA Tinubu ya ba kowanne Gwamna shinkafa tirela 20 a raba wa talakawa

Tinubu ya ba kowanne Gwamna shinkafa tirela 20 a raba wa talakawa

Gwamnatin Tarayya ta ayyana raba shinkafa tirela 20 ga jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja, domin rabawa ga mabukata.

Za a raba kayan abincin ne a faɗin kasar a masatyin wani matsaki na kawar da matsalar yunwa da ke addabar kasar.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan ga manema labaran fadar Shugaban Kasa a ranar Litinin, jim kadan bayan fitowa daga taron Majalisar Zartawa wanda Shugaban Kasar, Bola Tinubu ya jagoranta.

Ministan ya ce majalisar ta fahimci yadda matsalar karancin abincin ke addabar ’yan kasar, don hakan ta amince da raba shinkafa tirela 20 ga kowacce jiha da Abuja ga mabukata.

Al’ummar Nijeriya dai na fama da matsalar tsadar abinci, abin da suka alakanta da cire tallafin man fetur da gwamnatin Tinubu ta yi.

Matakin dai ya haifar da tashin farashin kayan masarufi da kayan amfanin yau da kullum a kasar da ke da arzikin man fetur da ma’adinan a karkashin kasa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp