Home DUNIYA Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin jihar Kano ta yi alƙawarin kammala aikin gyara dukkannin cibiyoyin koyar da sana,oin dogaro da Kai da kuma kirkire-kirkire Wanda tsohon Gwamna Rabi’u Musa kwankwaso ya Samar tun a shekarar 2011 a daukacin ƙananan hukumomi 44 da ke Kano.

Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin bikin ranar baje kolin fasahar matasa ta duniya da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake ƙaramar hukumar Dawakin kudu haɗin gwiwa da hukumar kula da ilimin ƙananan yara ta duniya UNESCO ta shirya.

Gwamnan ya ce yin riko da sana’o’in hannu zai taimaka wajen habaka tattalin arziki da Kuma samawa Matasa aikin yi.

Abba Kabir ya yi alkawarin samawa cibiyar da gidajen kwanan dalibai da biya musu kudin karatu da daukar nauyin kai su makaranta a kullum da kuma kulawa da walwalarsu.

Da ya ke jawabi a wajen taron karamin ministan ma’aikatar ci-gaban matasa Mista Ayodele Olawode ya yaba da harkokin cibiyar, inda ya ce ma’aikatar sa ta fito da wani shirin ilimantar da matasa miliyan 7 sana’o’in dogaro da kai.

Shugaban Hukumar UNESCO a Nijeriya Abdulrahman Diyalo ya ce za su yi haɗin gwiwa da gwamnatin kano da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote domin koyar da dubban matasa sana’o’in dogaro da kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp