Home DUNIYA ‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 150 tare da kashe 4...

‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 150 tare da kashe 4 a jihar Zamfara

Rahotannin daga jihar Zamfara na bayyana cewa ‘yan taádda masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa sun yi garkuwa da mutane 150 cikin su har da yara kanana a kauyen Dan isa dake karamar hukumar kaura Namoda dake jihar.

harin ya faru ne makwanni kadan bayan da ýan bindigara suka saki mutune 46 mazauna garin Dogon kade da suka saka bayan an biya kudin fansa naira miliyan 21.

dan isa dai gari ne dake da nisan kilomita 14 zuwa birnin jihar wato gusua.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito wani mazaunin garin da aka yi garkuwa da matarsa da dan Sa na tabbatar da aukuwar lamarin.

mutumin wanda ya bukaci a sakaye sunansa, ya ce ‘yan ta’addan sun tasamma garin ne kan babura kusan 150, kowannen su dauke da mutane uku, inda suka fara harbi a iska, abinda ya sa wasu cikin al’umma guduwa domin neman tsira.

“Matata, Na’imah da Da na dan watanni shida a duniya, Sudais, na cikin wadanda ”Yan ta’addan suka yi garkuwa da su, sai matar kanina, Aisha, da yaron ta dan watannin takwas, mata da yawa da kananan yara ýan binidgar sukayi garkuwa da su,” a cewar sa.

wani mzaunin garin Muhammad Auwal (ba sunansa na gaskiya kenan ba), ya ambaci cewa Hajiya Rakiya, matar Wamban Dan Isa, Alhaji Bello Halilu, da wasu mata ‘yan taáddan suka raunata a gidan Alhaji Halilu.

Aminu Bello Dan isa, wani mazaunin garin ya ce gungun ‘yan ta’addan dake karkashin dan bindiga Alhaji Shehu Bagiwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp