Home DUNIYA ‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 150 tare da kashe 4...

‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 150 tare da kashe 4 a jihar Zamfara

Rahotannin daga jihar Zamfara na bayyana cewa ‘yan taádda masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa sun yi garkuwa da mutane 150 cikin su har da yara kanana a kauyen Dan isa dake karamar hukumar kaura Namoda dake jihar.

harin ya faru ne makwanni kadan bayan da ýan bindigara suka saki mutune 46 mazauna garin Dogon kade da suka saka bayan an biya kudin fansa naira miliyan 21.

dan isa dai gari ne dake da nisan kilomita 14 zuwa birnin jihar wato gusua.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito wani mazaunin garin da aka yi garkuwa da matarsa da dan Sa na tabbatar da aukuwar lamarin.

mutumin wanda ya bukaci a sakaye sunansa, ya ce ‘yan ta’addan sun tasamma garin ne kan babura kusan 150, kowannen su dauke da mutane uku, inda suka fara harbi a iska, abinda ya sa wasu cikin al’umma guduwa domin neman tsira.

“Matata, Na’imah da Da na dan watanni shida a duniya, Sudais, na cikin wadanda ”Yan ta’addan suka yi garkuwa da su, sai matar kanina, Aisha, da yaron ta dan watannin takwas, mata da yawa da kananan yara ýan binidgar sukayi garkuwa da su,” a cewar sa.

wani mzaunin garin Muhammad Auwal (ba sunansa na gaskiya kenan ba), ya ambaci cewa Hajiya Rakiya, matar Wamban Dan Isa, Alhaji Bello Halilu, da wasu mata ‘yan taáddan suka raunata a gidan Alhaji Halilu.

Aminu Bello Dan isa, wani mazaunin garin ya ce gungun ‘yan ta’addan dake karkashin dan bindiga Alhaji Shehu Bagiwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp