Home General Kudurin kirkirar sarakuna 3 masu daraja ta 2 ya tsallake karatu a...

Kudurin kirkirar sarakuna 3 masu daraja ta 2 ya tsallake karatu a Majalisar Dokokin Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Kudurin kirkirar sarakuna masu daraja ta biyu ya tsallake karatun farko a majalisar dokokin Kano

Sabon kudurin ƙirƙirar sakaruna masu daraja ta biyu ya tsallake karatu na farko a zauren Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Sabbin Sarakunan da aka ƙirƙira dai sune na Rano, Ƙaraye da kuma Gaya.

A cewar ƙudurin, dukkansu za su kasance ne ƙarƙashin Sarkin Kano, wanda shi kaɗai ne mai daraja ta ɗaya yanzu a jihar.

Kananan hukumomin da za su kasance ƙarƙashin Sarkin Rano sune Rano Kibiya da Bunkure, shi kuma na Karaye yana da kananan hukumomin Karaye da Rogo.

Matakin na zuwa ne bayan Majalisar ta rushe dokar da ta kirkiri sabbin masarautu guda biyar a jihar ta shekara ta 2019, tare da rushe sarakunan da aka naɗa musu.

Daga bisani dai Gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II kan kujerarsa, inda ya sauke Aminu Ado Bayero da sauran sarakunan guda hudu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp