Home General Atiku ya zargi Tinubu da jefa Nijeriya cikin tsaka mai wuya

Atiku ya zargi Tinubu da jefa Nijeriya cikin tsaka mai wuya

Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa halin yunwa da ake ciki a Nijeriya manufofin gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu ne su ka haifar da shi babu gaira babu dalili.

Wannan na cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya fitar kuma aka raba ga manema labarai a Nijeriya, wadda ta dora alhakin yanayin komajin rayuwa da Al’ummar kasar ke ciki na tsadar kayan masarufi kan kudirin shugaba Tinubu.

Atiku ya ce rashin samar da matsaya kan mafi karancin albashi da zai yi dai-dai da yanayin rayuwar da ake ciki, zai zama mummunar barazana ga rayuwar ma’aikata da iyalen su a matakan gwamnatocin tarayya, jiha da kananan hukumomin kasar.

“Tun bayan da gwamnatin Tinubu ta janye tallafin man fetur ba zato ba tsammani ba kuma tanadi, da karya darajar Naira wanda shi ma ba tare da lakari da yanayin  tattalin arzikin kasar da ya dogara kachokan a kan shigo da abubuwan masarufi sarrafafu ko wanda za a sarrafa ba, rayuwar yan kasa ya shiga ma wuyacin hali”. A cewar Atiku Abubakar.

A yanzu shugaba Tinubu na shirin ciwo bashin dala biliyan 2 kari akan dala kusan biliyan 3 da rabi, wanda ba a san manufar cin bashin ba, inda zargi yai kwari cewar bashin na tabbatar da walwalar fadar gwamnatin tarayya ne da manyan jami’an gwamnatin.

Jagoran yan hamayyar ya ce Wannan mummunan bashin zai kara yawan bashin da ake bin kasar zuwa kusan kimanin dalar amurka billiyan 100 wannan zai kara ma gembo gishiri wajen ta’azzara mummunan halin da jama’a ke ciki. Wannan ba karamin bakin labari ba ne.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp