Home General Atiku ya zargi Tinubu da jefa Nijeriya cikin tsaka mai wuya

Atiku ya zargi Tinubu da jefa Nijeriya cikin tsaka mai wuya

Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa halin yunwa da ake ciki a Nijeriya manufofin gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu ne su ka haifar da shi babu gaira babu dalili.

Wannan na cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya fitar kuma aka raba ga manema labarai a Nijeriya, wadda ta dora alhakin yanayin komajin rayuwa da Al’ummar kasar ke ciki na tsadar kayan masarufi kan kudirin shugaba Tinubu.

Atiku ya ce rashin samar da matsaya kan mafi karancin albashi da zai yi dai-dai da yanayin rayuwar da ake ciki, zai zama mummunar barazana ga rayuwar ma’aikata da iyalen su a matakan gwamnatocin tarayya, jiha da kananan hukumomin kasar.

“Tun bayan da gwamnatin Tinubu ta janye tallafin man fetur ba zato ba tsammani ba kuma tanadi, da karya darajar Naira wanda shi ma ba tare da lakari da yanayin  tattalin arzikin kasar da ya dogara kachokan a kan shigo da abubuwan masarufi sarrafafu ko wanda za a sarrafa ba, rayuwar yan kasa ya shiga ma wuyacin hali”. A cewar Atiku Abubakar.

A yanzu shugaba Tinubu na shirin ciwo bashin dala biliyan 2 kari akan dala kusan biliyan 3 da rabi, wanda ba a san manufar cin bashin ba, inda zargi yai kwari cewar bashin na tabbatar da walwalar fadar gwamnatin tarayya ne da manyan jami’an gwamnatin.

Jagoran yan hamayyar ya ce Wannan mummunan bashin zai kara yawan bashin da ake bin kasar zuwa kusan kimanin dalar amurka billiyan 100 wannan zai kara ma gembo gishiri wajen ta’azzara mummunan halin da jama’a ke ciki. Wannan ba karamin bakin labari ba ne.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp