Sojojin Nijeriya sun kama ‘yan ta’adda biyu a jihar Taraba

Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta sami nasarar kama wasu ‘yan bindiga biyu a jihar Taraba da ke tsakiyar ƙasar tare da ƙwace babura daga hannunsu.

Wata sanarwa da mataimakin kakakin runudunar, Kanal Oni Olubodunde, ya fitar ta ce dakarun rundunar Operation Whirl Stroke ne suka yi nasarar kama mutanen da ba ta bayyana sunansu ba a ranar Alhamis.

“Samamen da dakaru suka kai bayan tattara bayanan sirri a ƙauyen Geshi na ƙaramar hukumar Donga a jihar Taraba ya yi sanadiyyar ƙwato babur biyu da ‘yanta’addan ke amfani da su,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa an samu bayanan sirrin ne bayan wasu mahara sun kai hari, inda dakaru suka ɗunguma zuwa Geshi kuma suka fara musayar wuta da su “abin da ya sa suka tsere zuwa cikin daji”.

“Yanzu haka ‘yanta’addan na hannunmu domin gudanar da bincike.”

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 10 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 52 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com