Home DUNIYA Atiku ya gargadi Tinubu kan tauye hakkin ‘yan Jaridu a Nijeriya

Atiku ya gargadi Tinubu kan tauye hakkin ‘yan Jaridu a Nijeriya

Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP a zaben shekara ta 2023 da ta gabata, Alhaji Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin jam’iyyar APC mai mulkin  karkashin jagorancin Bola Tinubu, na murkushe yancin yada labarai da kafafen yada labarai ke da shi kundin tsarin mulki kasa na 1999 da aka yiwa gyaran fuska.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya fitar kuma aka raba ga manema labarai. inda tace da ayyana yunkurin gwamnatin matsayin wata barazana ga harkokin yada labarai.

 

“Ba karamar barazana ba ce ga tabbatar da dimokaradiyyar Nijeriya, wadda ta ke damfare akan durakun bangarori guda hudu na zartarwa, dokoki, Shari’a da na yan jarida wadanda hakkin sanar da al’umma halin da kasa ta ke ciki ya rataya a wutansu”.

 

Atiku Ya yi kira ga yan jarida a kasar da cewa kada su bari wannan barazanar ta tsorata su, ta yadda zasu kasa sanar da al’umma rawar da gwamnatin da ke mulkinsu ke takawa wajen tasarrafi da al’amuran da suka shafi rayuwar su da walwalar su.

Idan za’a iya tunawa gwamnatin tarayyar Nijeriya na shan suka tun bayan da jaridar Daily Trust ta wallafa labarin kan batun yarjejeniyar Samoa da gwamantin Nijeriya, wadda ake zargin cewa akwai batun auren jinsi a cikin ta.

Lamarin da yasa gwamnatin tarayyar ta musanta, har ma ya ti barazanar daukar matakin Shari’a kan Kamfanin jaridar Daily Trust.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp