Home DUNIYA Atiku ya gargadi Tinubu kan tauye hakkin ‘yan Jaridu a Nijeriya

Atiku ya gargadi Tinubu kan tauye hakkin ‘yan Jaridu a Nijeriya

Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP a zaben shekara ta 2023 da ta gabata, Alhaji Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin jam’iyyar APC mai mulkin  karkashin jagorancin Bola Tinubu, na murkushe yancin yada labarai da kafafen yada labarai ke da shi kundin tsarin mulki kasa na 1999 da aka yiwa gyaran fuska.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya fitar kuma aka raba ga manema labarai. inda tace da ayyana yunkurin gwamnatin matsayin wata barazana ga harkokin yada labarai.

 

“Ba karamar barazana ba ce ga tabbatar da dimokaradiyyar Nijeriya, wadda ta ke damfare akan durakun bangarori guda hudu na zartarwa, dokoki, Shari’a da na yan jarida wadanda hakkin sanar da al’umma halin da kasa ta ke ciki ya rataya a wutansu”.

 

Atiku Ya yi kira ga yan jarida a kasar da cewa kada su bari wannan barazanar ta tsorata su, ta yadda zasu kasa sanar da al’umma rawar da gwamnatin da ke mulkinsu ke takawa wajen tasarrafi da al’amuran da suka shafi rayuwar su da walwalar su.

Idan za’a iya tunawa gwamnatin tarayyar Nijeriya na shan suka tun bayan da jaridar Daily Trust ta wallafa labarin kan batun yarjejeniyar Samoa da gwamantin Nijeriya, wadda ake zargin cewa akwai batun auren jinsi a cikin ta.

Lamarin da yasa gwamnatin tarayyar ta musanta, har ma ya ti barazanar daukar matakin Shari’a kan Kamfanin jaridar Daily Trust.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp