Home DUNIYA UAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya

UAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta dage haramcin shiga ƙasarta da ta yi wa ‘yan Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar wacce PRNigeria Hausa ta samu mai dauke da sa hannun Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai na Kasa, Mohammed Idris, a ranar Litinin.

Sanarwar ta ce bayan wata tattaunawa da gwamantin Nijeriyar ta yi da ta ƙasar, an sami cim ma matsaya da yarjejeniyar barin ‘yan Nijeriya su ci gaba da shiga kasar ta UAE.

Kazalika, sanarwar ta ce daga yarjejeniyar har da ɗage haramcin bayar da izinin shiga UAE ga dukkan ’yan Nijieriyar dake son shiga kasa

Sanarwar ta ce za a iya fara neman bizar daga 15 ga watan na Yuli, ta kuma bukaci ‘yan kasar su yi nazari kan bizar ta hanyar ziyartar shafinta na intanet domin karin bayani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp