Home General Atiku ya zargi Tinubu da jefa Nijeriya cikin tsaka mai wuya

Atiku ya zargi Tinubu da jefa Nijeriya cikin tsaka mai wuya

Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa halin yunwa da ake ciki a Nijeriya manufofin gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu ne su ka haifar da shi babu gaira babu dalili.

Wannan na cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya fitar kuma aka raba ga manema labarai a Nijeriya, wadda ta dora alhakin yanayin komajin rayuwa da Al’ummar kasar ke ciki na tsadar kayan masarufi kan kudirin shugaba Tinubu.

Atiku ya ce rashin samar da matsaya kan mafi karancin albashi da zai yi dai-dai da yanayin rayuwar da ake ciki, zai zama mummunar barazana ga rayuwar ma’aikata da iyalen su a matakan gwamnatocin tarayya, jiha da kananan hukumomin kasar.

“Tun bayan da gwamnatin Tinubu ta janye tallafin man fetur ba zato ba tsammani ba kuma tanadi, da karya darajar Naira wanda shi ma ba tare da lakari da yanayin  tattalin arzikin kasar da ya dogara kachokan a kan shigo da abubuwan masarufi sarrafafu ko wanda za a sarrafa ba, rayuwar yan kasa ya shiga ma wuyacin hali”. A cewar Atiku Abubakar.

A yanzu shugaba Tinubu na shirin ciwo bashin dala biliyan 2 kari akan dala kusan biliyan 3 da rabi, wanda ba a san manufar cin bashin ba, inda zargi yai kwari cewar bashin na tabbatar da walwalar fadar gwamnatin tarayya ne da manyan jami’an gwamnatin.

Jagoran yan hamayyar ya ce Wannan mummunan bashin zai kara yawan bashin da ake bin kasar zuwa kusan kimanin dalar amurka billiyan 100 wannan zai kara ma gembo gishiri wajen ta’azzara mummunan halin da jama’a ke ciki. Wannan ba karamin bakin labari ba ne.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp