Mun gano wadanda ke daukar nauyin Zanga – Zanga a Nijeriya – DSS

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya, DSS ta yi gargaɗi dangane da shirin zanga-zangar matsin rayuwa a kasar.

Hukumar ta DSS ta ce tuni ta riga ta gano waɗanda suka kitsa ta da masu goyon bayan zanga-zangar, inda suka gargaɗe su da su sanya kishin ƙasa su dakatar da shirin zanga-zangar.

Gargaɗin na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Dakta Peter Afunanya ya aike wa manema labarai. wadda ta ce hukumar ta DSS ta gano cewa wasu batagari na shirin karkatar da akalar zanga-zangar da manufar tayar da zaune tsaye a Najeriya.

Dakta Afunanya ya kuma yi zargin cewa burin masu kitsa zanga-zangar shi ne sauya gwamnati musamman ta tarayya.

“Masu kitsa zanga-zangar na son yin amfani da haddasa hatsaniya domin shafa wa gwamnatin tarayya da na jihohi kashin kaji da ɓata musu suna domin haɗa su da talakawa. Burinsu shi ne sauya gwamnati musamman ta tarayya.” In ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa ta duk da cewa ta gano masu kitsa zanga-zangar da masu ba su kuɗaɗe amma hukumar tana bin hanyoyin da doka ta tanada waɗanda ba na amfani da ƙarfi ba domin daƙile zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 23 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 5 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com