Home General Kada ku shiga cikin ‘yan fashi da makami da sunan zanga -zanga...

Kada ku shiga cikin ‘yan fashi da makami da sunan zanga -zanga – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya bayyana cewa baza su bari a gudnar da zanga –zanga da ake shirin farawa daya ga watan agusta a birnin ba, saboda ranar 1 ga watan Agusta rana ce ta karrama sarakunan gargajiya a birnin.

Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai bayan kamala taron tsaron birnin, wanda ya sami halartar karamar ministan birnin. Dr. Mariya Bunkure, jamián hukumar dake lura da birnin ta FCTA, shuwagabannin kananan hukumomi da sauran jamián tsaro a birnin.

Ministan ya bayyana cewa a wannan rana suna sa ran ziyartar aikin hanyar Saburi dake kusa da Dei-Dei a cikin kwaryar birnin na Abuja wato Abuja Municipal Area Council (AMAC), in da ya bukaci mazauna yankin kada su shiga cikin ýan fashi da makami don gudanar da zanga zanga.

“ka da ku bi wadannan ýan fashin da makami kan hanya, wadanda ke ikirarin gudanar da zanga –zanga. Babu wani abu zanga zanga. Abuja baza ta zama guda cikin yankunan da za’a gudanar da ita ba. Abinda kuke bukata shine shugabanci na gari, kuma muna yi muku abinda kuke bukata,’’

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp